Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe
Published: July 22, 2026 at 2:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah Kautal Hore a jihar Gombe ta bayyana goyon bayanta ga Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna, wanda aka fi sani da Sardaunan Gombe, a matsayin ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC a zaɓen shekarar 2027

Shugaban ƙungiyar a jihar, Ardo Chindo Abubakar, ne ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da makiyaya da manoma a Masarautar Bojude da ke Ƙaramar Hukumar Kwami.

Taron ya gudana ne a lokacin da tawagar yaƙin neman goyon bayan Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna ƙarƙashin jagorancin Dakta Ahmad Muhammad Gana ta kai ziyara yankin

Ardo Chindo ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma tare da samar da mafita ga rikice-rikicen da suka daɗe suna faruwa tsakanin al’ummomin Fulani a yankin. Ya kuma buƙaci mazauna yankin su ci gaba da zama lafiya domin samun ci gaba mai ɗorewa.

Da yake jawabi, jagoran tawagar yaƙin neman goyon baya, Dakta Ahmad Gana, ya bayyana Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin mutum mai tawali’u, tausayi da ƙwarewa wajen gudanar da aiki. Ya ce ya taimaka wa mutane da dama a lokacin da yake aiki a Hukumar Samar da Ruwa ta Jihar Gombe da kuma Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO).

Ya yi kira ga al’ummar jihar Gombe da su marawa Dakta Gwamna baya, yana mai cewa jajircewarsa, gaskiyarsa da sadaukarwarsa wajen taimakon talakawa sun cancanci a ba shi damar jagorantar jihar.

Shi ma Shugaban Hukumar Ci Gaban Ƙaramar Hukumar Kwami ta Yamma (Kwami West LCDA), Sa’ad Abdulmumini, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar APC da ‘yan takararta, yana mai cewa ayyukan ci gaban da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya aiwatar sun ƙara wa jam’iyyar karɓuwa a wajen al’umma.

A nasa jawabin, Hakimin Bojude, Alhaji Muhammad Ibrahim Dan Buram, ya lissafo wasu ayyukan raya ƙasa da aka aiwatar a masarautarsa, ciki har da gina fadar hakimi, hanyoyi, fitilun tituna masu amfani da hasken rana da kuma kafa hedikwatar Hukumar Ci Gaban Ƙaramar Hukumar Kwami ta Yamma a Bojude.

Hakimin ya sake jaddada goyon bayansa ga Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna da sauran ‘yan takarar APC, yana mai bayyana fatan cewa za su ci gaba da kawo ribar dimokuraɗiyya ga al’ummar Jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa
Next Post: An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka
Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Isra’ila Zata Rusa Gidajen Da Suke Iyakarta Da Lebanon Labarai
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.