Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe
Published: July 22, 2026 at 2:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah Kautal Hore a jihar Gombe ta bayyana goyon bayanta ga Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna, wanda aka fi sani da Sardaunan Gombe, a matsayin ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC a zaɓen shekarar 2027

Shugaban ƙungiyar a jihar, Ardo Chindo Abubakar, ne ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da makiyaya da manoma a Masarautar Bojude da ke Ƙaramar Hukumar Kwami.

Taron ya gudana ne a lokacin da tawagar yaƙin neman goyon bayan Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna ƙarƙashin jagorancin Dakta Ahmad Muhammad Gana ta kai ziyara yankin

Ardo Chindo ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma tare da samar da mafita ga rikice-rikicen da suka daɗe suna faruwa tsakanin al’ummomin Fulani a yankin. Ya kuma buƙaci mazauna yankin su ci gaba da zama lafiya domin samun ci gaba mai ɗorewa.

Da yake jawabi, jagoran tawagar yaƙin neman goyon baya, Dakta Ahmad Gana, ya bayyana Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin mutum mai tawali’u, tausayi da ƙwarewa wajen gudanar da aiki. Ya ce ya taimaka wa mutane da dama a lokacin da yake aiki a Hukumar Samar da Ruwa ta Jihar Gombe da kuma Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO).

Ya yi kira ga al’ummar jihar Gombe da su marawa Dakta Gwamna baya, yana mai cewa jajircewarsa, gaskiyarsa da sadaukarwarsa wajen taimakon talakawa sun cancanci a ba shi damar jagorantar jihar.

Shi ma Shugaban Hukumar Ci Gaban Ƙaramar Hukumar Kwami ta Yamma (Kwami West LCDA), Sa’ad Abdulmumini, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar APC da ‘yan takararta, yana mai cewa ayyukan ci gaban da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya aiwatar sun ƙara wa jam’iyyar karɓuwa a wajen al’umma.

A nasa jawabin, Hakimin Bojude, Alhaji Muhammad Ibrahim Dan Buram, ya lissafo wasu ayyukan raya ƙasa da aka aiwatar a masarautarsa, ciki har da gina fadar hakimi, hanyoyi, fitilun tituna masu amfani da hasken rana da kuma kafa hedikwatar Hukumar Ci Gaban Ƙaramar Hukumar Kwami ta Yamma a Bojude.

Hakimin ya sake jaddada goyon bayansa ga Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna da sauran ‘yan takarar APC, yana mai bayyana fatan cewa za su ci gaba da kawo ribar dimokuraɗiyya ga al’ummar Jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa
Next Post: An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
  • Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
  • Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
  • “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.