Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu
Published: December 22, 2025 at 5:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutane 9 sun rasa rayukansu, wasu akalla 10 suka ji rauni a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka bude wuta kan wata mashaya da asubahin lahadi a kasar Afirka ta Kudu.

Wannan lamarin ya faru da misalin karfe 1 na dare a garin bakar fata na Bekkersdal dake da tazarar kilomita 46 a yamma da birnin Johannesburg, wannan shine mummunan harin bindiga na biyu da aka kai cikin kasar a makonni ukun da suka shige.

Wasu ’yan bindiga su 12 cikin wasu moto biyu, sun bude wuta a kan mutanen dake shakatawa a wannan mashaya mai suna KwaNoxolo dake unguwar Tambo a garin na Bekkersdal, suka kuma ci gaba da bude wuta kan jama’a a yayin da suke tserewa daga wurin.

‘Yan sandan Afirka ta Kudu suka ce wasu daga cikin mutanen suna tafiyarsu ne kawai a kan titi a lokacin da ‘yan bindigar suka bude musu wuta.

Kwamishinan lardi mai kula da Gauteng, MNanjo janar Fred kekana, ya shaidawa kamfanin dillancin labaran AP a wurin da wannan lamari ya faru cewa ‘yan bindigar, wadanda wasunsu suka rufe kai da fuskarsu da kyalle, sun yi amfani da bindiga samfurin AK-47 guda daya da wasu kananan bindigogi da yawa.

‘Yan sanda ba su bayar da bayanin mutanen da aka kashe ko aka raunata ba, amma kakakin rundunar sandan, Birgediya Brenda Muridili, ta ce akwai wani direban tasi wanda ya ajiye fasinja ke nan zai bar wurin sai maharan suka rutsa da shi, kuma suka kashe shi.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su
Next Post: Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi Labarai
  • Alhinin Rasuwar Bello Sharada, Fitaccen Mai Sharhi Kan Siyasar Najeriya Afrika
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.