Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
Published: May 28, 2026 at 2:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC domin tunkarar babban zaben kasa mai zuwa, inda ya bayyana kudirinsa na jagorantar yunkurin farfado da dimokuradiyya, tsaro da tattalin arzikin Najeriya.

Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin wanda zai wakilci jam’iyyar a zaben shugaban kasa, Atiku ya bayyana godiyarsa ga shugabanni da mambobin ADC bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya ce jam’iyyar ADC ta nuna cewa dimokuradiyya na nan daram a Najeriya, duk da abin da ya kira matsin lamba da takurawa jam’iyyun adawa daga gwamnatin APC mai mulki.

Atiku ya ce a cikin ADC ana bai wa mambobi damar bayyana ra’ayoyinsu da fafatawa cikin gaskiya da adalci, yana mai cewa hakan ya bambanta da yadda ake gudanar da siyasa a yanzu.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya zargi gwamnatin tarayya da haddasa rikice-rikice a jam’iyyun adawa ta hanyar amfani da hukumomin gwamnati da wasu bangarori na shari’a.

Ya kuma yi Allah wadai da ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, , yana mai cewa ana amfani da tsare-tsare irin haka wajen tsoratar da ‘yan adawa.

Atiku ya ce gwamnatin ADC idan ta hau mulki za ta dauki matakai masu tsauri wajen magance matsalar rashin tsaro ta hanyar karfafa rundunonin tsaro, samar da kayan aiki na zamani, horas da jami’ai da kuma inganta walwalarsu.

A bangaren ilimi kuwa, ya yi alkawarin samar da ilimin firamare da sakandare kyauta tare da bai wa matasa horo kan fasahar zamani, kirkire-kirkire da sana’o’i domin rage zaman banza da rashin aikin yi.

Dangane da tattalin arziki, Atiku ya soki gwamnatin APC kan yadda talauci da wahalar rayuwa suka karu a kasar, yana mai cewa gwamnatin sa za ta mayar da hankali wajen samar da ci gaban tattalin arziki mai anfani ga daukacin ‘yan Najeriya.

Ya kuma yi alkawarin ba bangaren lafiya muhimmanci ta hanyar kara zuba jari a cibiyoyin kiwon lafiya da samar da asibitoci na zamani domin rage tafiye-tafiyen neman magani zuwa kasashen waje.

Atiku ya yi kira ga dukkan mambobin jam’iyyar da sauran ‘yan siyasa masu kishin kasa da su hada kai domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a babban zaben kasa mai zuwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
Next Post: Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Karin Labarai Masu Alaka

Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
  • Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
  • Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.