Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika

Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
Published: May 28, 2026 at 2:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC domin tunkarar babban zaben kasa mai zuwa, inda ya bayyana kudirinsa na jagorantar yunkurin farfado da dimokuradiyya, tsaro da tattalin arzikin Najeriya.

Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin wanda zai wakilci jam’iyyar a zaben shugaban kasa, Atiku ya bayyana godiyarsa ga shugabanni da mambobin ADC bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya ce jam’iyyar ADC ta nuna cewa dimokuradiyya na nan daram a Najeriya, duk da abin da ya kira matsin lamba da takurawa jam’iyyun adawa daga gwamnatin APC mai mulki.

Atiku ya ce a cikin ADC ana bai wa mambobi damar bayyana ra’ayoyinsu da fafatawa cikin gaskiya da adalci, yana mai cewa hakan ya bambanta da yadda ake gudanar da siyasa a yanzu.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya zargi gwamnatin tarayya da haddasa rikice-rikice a jam’iyyun adawa ta hanyar amfani da hukumomin gwamnati da wasu bangarori na shari’a.

Ya kuma yi Allah wadai da ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, , yana mai cewa ana amfani da tsare-tsare irin haka wajen tsoratar da ‘yan adawa.

Atiku ya ce gwamnatin ADC idan ta hau mulki za ta dauki matakai masu tsauri wajen magance matsalar rashin tsaro ta hanyar karfafa rundunonin tsaro, samar da kayan aiki na zamani, horas da jami’ai da kuma inganta walwalarsu.

A bangaren ilimi kuwa, ya yi alkawarin samar da ilimin firamare da sakandare kyauta tare da bai wa matasa horo kan fasahar zamani, kirkire-kirkire da sana’o’i domin rage zaman banza da rashin aikin yi.

Dangane da tattalin arziki, Atiku ya soki gwamnatin APC kan yadda talauci da wahalar rayuwa suka karu a kasar, yana mai cewa gwamnatin sa za ta mayar da hankali wajen samar da ci gaban tattalin arziki mai anfani ga daukacin ‘yan Najeriya.

Ya kuma yi alkawarin ba bangaren lafiya muhimmanci ta hanyar kara zuba jari a cibiyoyin kiwon lafiya da samar da asibitoci na zamani domin rage tafiye-tafiyen neman magani zuwa kasashen waje.

Atiku ya yi kira ga dukkan mambobin jam’iyyar da sauran ‘yan siyasa masu kishin kasa da su hada kai domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a babban zaben kasa mai zuwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
Next Post: Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Karin Labarai Masu Alaka

Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
  • Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
  • Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.