Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
Published: May 28, 2026 at 2:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC domin tunkarar babban zaben kasa mai zuwa, inda ya bayyana kudirinsa na jagorantar yunkurin farfado da dimokuradiyya, tsaro da tattalin arzikin Najeriya.

Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin wanda zai wakilci jam’iyyar a zaben shugaban kasa, Atiku ya bayyana godiyarsa ga shugabanni da mambobin ADC bisa amincewar da suka nuna masa.

Ya ce jam’iyyar ADC ta nuna cewa dimokuradiyya na nan daram a Najeriya, duk da abin da ya kira matsin lamba da takurawa jam’iyyun adawa daga gwamnatin APC mai mulki.

Atiku ya ce a cikin ADC ana bai wa mambobi damar bayyana ra’ayoyinsu da fafatawa cikin gaskiya da adalci, yana mai cewa hakan ya bambanta da yadda ake gudanar da siyasa a yanzu.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya zargi gwamnatin tarayya da haddasa rikice-rikice a jam’iyyun adawa ta hanyar amfani da hukumomin gwamnati da wasu bangarori na shari’a.

Ya kuma yi Allah wadai da ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, , yana mai cewa ana amfani da tsare-tsare irin haka wajen tsoratar da ‘yan adawa.

Atiku ya ce gwamnatin ADC idan ta hau mulki za ta dauki matakai masu tsauri wajen magance matsalar rashin tsaro ta hanyar karfafa rundunonin tsaro, samar da kayan aiki na zamani, horas da jami’ai da kuma inganta walwalarsu.

A bangaren ilimi kuwa, ya yi alkawarin samar da ilimin firamare da sakandare kyauta tare da bai wa matasa horo kan fasahar zamani, kirkire-kirkire da sana’o’i domin rage zaman banza da rashin aikin yi.

Dangane da tattalin arziki, Atiku ya soki gwamnatin APC kan yadda talauci da wahalar rayuwa suka karu a kasar, yana mai cewa gwamnatin sa za ta mayar da hankali wajen samar da ci gaban tattalin arziki mai anfani ga daukacin ‘yan Najeriya.

Ya kuma yi alkawarin ba bangaren lafiya muhimmanci ta hanyar kara zuba jari a cibiyoyin kiwon lafiya da samar da asibitoci na zamani domin rage tafiye-tafiyen neman magani zuwa kasashen waje.

Atiku ya yi kira ga dukkan mambobin jam’iyyar da sauran ‘yan siyasa masu kishin kasa da su hada kai domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a babban zaben kasa mai zuwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
Next Post: Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Jana’izar Jagoran Ƙolin Iran Ta Kawo Tsauraran Matakan Tsaro A Tehran Afrika
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.