Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce gwamnatinsa ta samu nasarar shimfiɗa tubalin farfaɗo da tattalin arziki da sake daidaita al’amuran ƙasa bayan shekaru uku da hawansa mulki.
Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar domin cika shekara uku cif na gwamnatin sa a ranar 29 ga watan Mayun 2026.
Shugaban ƙasar ya ce lokacin da ya karɓi mulki a shekarar 2023, Najeriya na fuskantar matsin tattalin arziki, ƙarancin kudaden shiga, matsalar tsaro da kuma tabarbarewar harkokin gwamnati.
Ya ce gwamnatinsa ta ɗauki matakai masu wahala amma masu muhimmanci domin ceto ƙasar daga durƙushewar tattalin arziki, ciki har da cire tallafin man fetur da kuma gyaran tsarin musayar kuɗaɗen waje.
A cewarsa, Najeriya na kashe kusan naira biliyan 18.4 a kullum wajen tallafin man fetur kafin cire shi, lamarin da ya ce yana hana zuba jari a bangarorin raya ƙasa kamar hanyoyi, lafiya da ilimi.
Tinubu ya amince cewa matakan da gwamnatin ta ɗauka sun jawo tsadar rayuwa da wahalhalu ga jama’a, amma ya jaddada cewa sadaukarwar da ’yan Najeriya suka yi ba ta tafi a banza ba.
“Yanzu Najeriya ta fara samun daidaito kuma tana ci gaba a hankali,” in ji shi.
Shugaban ƙasar ya bayyana cewa tattalin arzikin Najeriya ya kara ƙarfi idan aka kwatanta da shekarar 2023, yana mai cewa kasuwar hannayen jari ta ƙaru daga naira tiriliyan 30 zuwa tiriliyan 160.
Ya kuma ce gwamnatin sa na gudanar da manyan ayyukan hanyoyi sama da kilomita 2,700 a faɗin ƙasar nan, ciki har da titin Lagos-Calabar Coastal Highway, Sokoto-Badagry Super Highway da kuma hanyar Abuja zuwa Kano.
A bangaren mai da gas, Tinubu ya ce gyare-gyaren da gwamnati ta yi sun jawo sabbin jarin biliyoyin daloli tare da bunƙasa matatun mai na cikin gida domin rage dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje.
Game da wutar lantarki, shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa na ƙoƙarin magance matsalolin da suka dabaibaye bangaren tsawon shekaru ta hanyar inganta layukan sadar da wuta da kuma zuba jari a makamashi.
A bangaren noma kuwa, ya ce gwamnati ta tallafa wa miliyoyin manoma da iri, taki, injina da hanyoyin samun rance domin bunƙasa samar da abinci da rage tsadar rayuwa.
Tinubu ya kuma bayyana cewa Asusun Lamunin Dalibai na Najeriya ya taimaka wa sama da dalibai miliyan 1.5 da kudade sama da naira biliyan 282 domin ci gaba da karatu.
Haka kuma ya ce gwamnati na ci gaba da gina gidaje masu araha a jihohi daban-daban tare da samar da dubban ayyukan yi ga matasa.
Dangane da tsaro, shugaban ƙasar ya ce jami’an tsaro sun ƙara kaimi wajen yaki da ’yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka, yana mai cewa an fara samun saukin matsalar tsaro a wasu yankuna.
Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da haɗa kai tare da nuna haƙuri da fatan alheri ga ƙasa.
“Dole mu fifita haɗin kai a kan rarrabuwar kawuna, da fata mai kyau a kan yanke ƙauna,” in ji shugaban ƙasar.
Tinubu ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ƙoƙarin rage tsadar rayuwa tare da samar da karin damammakin ayyukan yi da bunƙasa kasuwanci.


