Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi
Published: May 29, 2026 at 9:54 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce gwamnatinsa ta samu nasarar shimfiɗa tubalin farfaɗo da tattalin arziki da sake daidaita al’amuran ƙasa bayan shekaru uku da hawansa mulki.

Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar domin cika shekara uku cif na gwamnatin sa a ranar 29 ga watan Mayun 2026.

Shugaban ƙasar ya ce lokacin da ya karɓi mulki a shekarar 2023, Najeriya na fuskantar matsin tattalin arziki, ƙarancin kudaden shiga, matsalar tsaro da kuma tabarbarewar harkokin gwamnati.

Ya ce gwamnatinsa ta ɗauki matakai masu wahala amma masu muhimmanci domin ceto ƙasar daga durƙushewar tattalin arziki, ciki har da cire tallafin man fetur da kuma gyaran tsarin musayar kuɗaɗen waje.

A cewarsa, Najeriya na kashe kusan naira biliyan 18.4 a kullum wajen tallafin man fetur kafin cire shi, lamarin da ya ce yana hana zuba jari a bangarorin raya ƙasa kamar hanyoyi, lafiya da ilimi.

Tinubu ya amince cewa matakan da gwamnatin ta ɗauka sun jawo tsadar rayuwa da wahalhalu ga jama’a, amma ya jaddada cewa sadaukarwar da ’yan Najeriya suka yi ba ta tafi a banza ba.

“Yanzu Najeriya ta fara samun daidaito kuma tana ci gaba a hankali,” in ji shi.

Shugaban ƙasar ya bayyana cewa tattalin arzikin Najeriya ya kara ƙarfi idan aka kwatanta da shekarar 2023, yana mai cewa kasuwar hannayen jari ta ƙaru daga naira tiriliyan 30 zuwa tiriliyan 160.

Ya kuma ce gwamnatin sa na gudanar da manyan ayyukan hanyoyi sama da kilomita 2,700 a faɗin ƙasar nan, ciki har da titin Lagos-Calabar Coastal Highway, Sokoto-Badagry Super Highway da kuma hanyar Abuja zuwa Kano.

A bangaren mai da gas, Tinubu ya ce gyare-gyaren da gwamnati ta yi sun jawo sabbin jarin biliyoyin daloli tare da bunƙasa matatun mai na cikin gida domin rage dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje.

Game da wutar lantarki, shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa na ƙoƙarin magance matsalolin da suka dabaibaye bangaren tsawon shekaru ta hanyar inganta layukan sadar da wuta da kuma zuba jari a makamashi.

A bangaren noma kuwa, ya ce gwamnati ta tallafa wa miliyoyin manoma da iri, taki, injina da hanyoyin samun rance domin bunƙasa samar da abinci da rage tsadar rayuwa.

Tinubu ya kuma bayyana cewa Asusun Lamunin Dalibai na Najeriya ya taimaka wa sama da dalibai miliyan 1.5 da kudade sama da naira biliyan 282 domin ci gaba da karatu.

Haka kuma ya ce gwamnati na ci gaba da gina gidaje masu araha a jihohi daban-daban tare da samar da dubban ayyukan yi ga matasa.

Dangane da tsaro, shugaban ƙasar ya ce jami’an tsaro sun ƙara kaimi wajen yaki da ’yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka, yana mai cewa an fara samun saukin matsalar tsaro a wasu yankuna.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da haɗa kai tare da nuna haƙuri da fatan alheri ga ƙasa.

“Dole mu fifita haɗin kai a kan rarrabuwar kawuna, da fata mai kyau a kan yanke ƙauna,” in ji shugaban ƙasar.

Tinubu ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ƙoƙarin rage tsadar rayuwa tare da samar da karin damammakin ayyukan yi da bunƙasa kasuwanci.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
Next Post: Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki Afrika
  • Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.