Majalisar Ƙolin Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NSCIA) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki matakan gaggawa domin magance abin da ta bayyana a matsayin hare-haren nuna wariya da kuma tauye haƙƙin Musulmi a sassa daban-daban na ƙasar nan.
Majalisar ta bayyana cewa idan ba a ɗauki matakan da suka dace ba cikin gaggawa, hakan na iya haifar da ƙarin damuwa da rashin gamsuwa a tsakanin al’ummar Musulmi.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na NSCIA, Abbas Jimoh, ya fitar a madadin majalisar, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Sarkin Musulmi na Najeriya, Mai Alfarma Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar.
A cikin sanarwar, majalisar ta nuna damuwa kan abin da ta ce na ci gaba da faruwa na nuna wariya ga Musulmi da kuma tauye musu wasu haƙƙoƙi da kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanadar.
NSCIA ta jaddada cewa Najeriya ƙasa ce da ke bai wa kowane ɗan ƙasa damar gudanar da addininsa cikin walwala da ‘yanci, don haka ya zama wajibi gwamnati da hukumomin tsaro su tabbatar da kare waɗannan haƙƙoƙi ba tare da nuna bambanci ba.
Majalisar ta kuma yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da bincike kan duk wasu korafe-korafe da suka shafi tauye ‘yancin addini tare da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da adalci da zaman lafiya.
NSCIA ta ce tana sa ran gwamnati za ta yi abin da ya dace cikin gaggawa domin kare haɗin kai da zaman lafiya a ƙasa, tare da tabbatar da cewa an mutunta haƙƙin kowane ɗan ƙasa ba tare da la’akari da addininsa ko asalinsa ba.


