Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai
Published: April 2, 2026 at 9:02 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ya yi mu’amala da wasu wakilai ta hanyar masu shiga tsakani daga ƙasar Pakistan game da rikicin Iran har zuwa ranar Talata, a cewar wani mutum da ke da masaniya game da lamarin wanda ya shaida wa Reuters. Wannan na nuna yadda rawarsa ke ƙara faɗaɗa wajen ƙoƙarin samar da mafita don kawo ƙarshen rikicin.

Bisa umarnin Shugaba Donald Trump, Vance ya aika da saƙo a ɓoye cewa Trump yana buɗe ƙofa ga tsagaita wuta muddin an cika wasu buƙatun Amurka, kamar yadda majiyar ta shaida wa Reuters a ranar Laraba.

Haka kuma Vance ya isar da abin da majiyar ta bayyana a matsayin “saƙo mai tsauri,” inda ya nuna cewa Trump ya fara gajiya da jinkiri, tare da gargadin cewa za a ƙara matsa lamba kan muhimman ababen more rayuwa na Iran idan Tehran ba ta amince da yarjejeniyar ba.

Majiyar ta ƙara da cewa ƙasar Pakistan na taka rawa a matsayin mai shiga tsakani tsakanin Amurka da Iran.

Vance na taka muhimiyar rawa wajen ƙoƙarin tattaunawa domin kawo ƙarshen yaƙin, wanda yanzu ya shiga mako na biyar.

Ana kallon sa a matsayin wanda zai iya gadan Trump a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2028, kuma ya ɗauki matakin taka-tsantsan game da rikicin, wanda ya dace da ra’ayinsa na dogon lokaci na nuna shakku kan tsawaita shiga harkokin sojan Amurka a ƙasashen waje.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa
Next Post: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah

Karin Labarai Masu Alaka

Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
“Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai Amurka
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.