Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
Published: January 14, 2026 at 3:33 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 14, 2026

Shugaban kungiyoyin Magoya Bayan Kwallon Kafa ta Najeriya reshen jihar Bauchi Alh Kabiru Ahmed Vice ya ce Najeriya zata iya samun nasara akan Ƙasar Moroko AFCON 2025.

Alh Kabiru Ahmed Vice ya ce la’akari da yadda tawagar Najeriya suka taka rawar gani a Wasanni su na baya a gasar cin kofin kasashen Afirka tun daga matakin rukuni har zuwa kwata final, haka na nuna cewar zata iya doke masu masaukin baki ƙasar Moroko a wasan da zasuyi na dab da Karshe.

Dukkanin Ƙasashen Afirka da suka je gasar babu wacce ta jefa yawan kwallaye a raga kamar Super Eagles, ” in ji shi.

Wannan ya na da nasaba da irin hazikan yan wasa da suke da su wadda suke fafata a manyan kungiyoyin kwallon kafa ta kasashen turai cikin su hadda wadda suka taba zama Gwarzayen kwallon kafa na afirka guda 2, Victor Osimhen da Ademola Lookman, ganinsu ya kara wa wasu ‘yan wasan karfin guiwa.

Ya ce duk da cewa Ƙasar Moroko ita ce mai masaukin baki ta na da dubban magoya baya a filin hakan ba zai ba ‘yan wasan Najeriya tsoro ba saboda sun goge da irin wannan abu tun a Turai.

Har ila Yau Kabiru yayi kira ga hukumar kwallon kafa ta Najeriya da ta rinka kulawa da walwalan ‘yan wasa da magoya baya don hakan shine zai kara musu kwarin guiwar yin abunda ya dace.

Duk da cewa wannan karon hukumar kwallon kafa ta Najeriya bata mara baya wa bangaren magoya baya don zuwa gasar cin kofin kasashen Afirka da ke guda na a kasar Moroko ba amman suna iya abun da zasuyi don ganin an samu nasara in ji Kabiru.

Saboda haka yayi kira ga gwamnati da masu hanu da shuni da su rinka tallafawa wajan ganin magoya baya suna hallartar irin wa’yannan gasar.

Daga karshe yayi fatan Najeriya zata lashe wannan kofin kasashen Afirka don huce haushin rashin zuwa gasar cin kofin Duniya.

A yau Laraba ne Ƙasar Najeriya zata buga da ƙasar Moroko a matakin wasan dab da Karshe na gasar cin kofin kasashen Afirka AFCON 2025, da ke gudana a can Moroko.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
Next Post: Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026 Wasanni
Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika
  • Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.