Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
Published: January 14, 2026 at 3:33 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 14, 2026

Shugaban kungiyoyin Magoya Bayan Kwallon Kafa ta Najeriya reshen jihar Bauchi Alh Kabiru Ahmed Vice ya ce Najeriya zata iya samun nasara akan Ƙasar Moroko AFCON 2025.

Alh Kabiru Ahmed Vice ya ce la’akari da yadda tawagar Najeriya suka taka rawar gani a Wasanni su na baya a gasar cin kofin kasashen Afirka tun daga matakin rukuni har zuwa kwata final, haka na nuna cewar zata iya doke masu masaukin baki ƙasar Moroko a wasan da zasuyi na dab da Karshe.

Dukkanin Ƙasashen Afirka da suka je gasar babu wacce ta jefa yawan kwallaye a raga kamar Super Eagles, ” in ji shi.

Wannan ya na da nasaba da irin hazikan yan wasa da suke da su wadda suke fafata a manyan kungiyoyin kwallon kafa ta kasashen turai cikin su hadda wadda suka taba zama Gwarzayen kwallon kafa na afirka guda 2, Victor Osimhen da Ademola Lookman, ganinsu ya kara wa wasu ‘yan wasan karfin guiwa.

Ya ce duk da cewa Ƙasar Moroko ita ce mai masaukin baki ta na da dubban magoya baya a filin hakan ba zai ba ‘yan wasan Najeriya tsoro ba saboda sun goge da irin wannan abu tun a Turai.

Har ila Yau Kabiru yayi kira ga hukumar kwallon kafa ta Najeriya da ta rinka kulawa da walwalan ‘yan wasa da magoya baya don hakan shine zai kara musu kwarin guiwar yin abunda ya dace.

Duk da cewa wannan karon hukumar kwallon kafa ta Najeriya bata mara baya wa bangaren magoya baya don zuwa gasar cin kofin kasashen Afirka da ke guda na a kasar Moroko ba amman suna iya abun da zasuyi don ganin an samu nasara in ji Kabiru.

Saboda haka yayi kira ga gwamnati da masu hanu da shuni da su rinka tallafawa wajan ganin magoya baya suna hallartar irin wa’yannan gasar.

Daga karshe yayi fatan Najeriya zata lashe wannan kofin kasashen Afirka don huce haushin rashin zuwa gasar cin kofin Duniya.

A yau Laraba ne Ƙasar Najeriya zata buga da ƙasar Moroko a matakin wasan dab da Karshe na gasar cin kofin kasashen Afirka AFCON 2025, da ke gudana a can Moroko.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
Next Post: Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi

Karin Labarai Masu Alaka

Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Arsenal Ta Fara Kare Kambun Gasar Premier League Da Ci 3-0 A Kan Coventry City Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NFF, Ta Umarci Tawagar Masu Horas Da Super Falcons Su Sauka Daga Bakin Aiki Nan Take Wasanni
  • Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
  • Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
  • Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.