NFF TA UMARNI KOCI NA SUPER FALCONS SU SAUƘA DAGA AIKI
Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya, NFF, ta umarci tawagar masu horas da Super Falcons da su sauka daga bakin aiki nan take, biyo bayan rashin gamsasshen sakamakon da ƙungiyar ta samu a gasar WAFCON ta 2026.
Super Falcons, wadda ta shiga gasar a matsayin zakarar da ke kare kambunta, ta fice daga gasar ne a matakin daf da na kusa da na ƙarshe bayan da Kamaru ta doke ta a wasan daf da na kusa da na ƙarshe.
Bayan ficewarta daga WAFCON, Super Falcons ta kuma samu koma baya a yunkurinta na samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta mata ta 2027.
A halin yanzu, NFF ba ta sanar da sabon tsarin horas da ƙungiyar ko wanda zai maye gurbin tawagar da ta sauka ba.
Super Falcons dai na daga cikin ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na mata mafi nasara a Afirka, inda Najeriya ta lashe kambun WAFCON sau 10.
Masu ruwa da tsaki a ƙwallon ƙafar Najeriya na sa ran NFF za ta gaggauta ɗaukar matakin da ya dace domin sake tsara tawagar da kuma shirya ta domin wasannin da ke gabanta.


