Alkalin wasan Somalia Omar Artan, wanda aka hana shi shiga ƙasar Amurka don yin alkalancin gasar cin kofin duniya, an zabe shi domin ya jagoranci wasan cin kofin Uefa Super Cup tsakanin Paris St-Germain da Aston Villa a wannan bazarar.
An shirya fafatawar tsakanin PSG, wacce ta lashe gasar zakarun Turai a kakar wasa ta bara da Aston Villa, wacce ta yi nasara a gasar Europa League, wasan za ta gudana a ranar 12 ga Agusta a Salzburg.
A cikin wata sanarwa, hukumar kula da kwallon kafa ta Turai ta ce an yanke wannan shawara ne bayan tattaunawa da Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (Caf).
Shugaban Uefa Aleksander Ceferin ya ce: “Omar Artan ƙwararren alkalin wasa ne, wanda ya tabbatar da kansa a matakin gasa mafi girma a Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka.
“An yi ƙwallon ƙafa ne don haɗa mutane, kuma Uefa tana son nuna girmamawa ga Omar da ƙwarewarsa ta yin alkalanci, wanda hakan ya sa ya sami wannan matsayi mai daraja.
“Ina godiya ga abokina shugaban Caf Patrice Motsepe saboda goyon bayan da himma.”
Artan, wanda ya lashe kyautar alkalan wasa na maza na Caf a shekarar 2025, wm ya kasance cikin jerin alkalan wasa na duniya na Fifa tun 2018, inda ya zama dan kasar Somaliya na farko da zai yi alkalanci a gasar cin kofin duniya.
Duk da haka, jami’an kan iyaka a Miami sun ki amincewa da shi duk da cewa yana da fasfo na diflomasiyya da kuma takardar izinin shiga Amurka sau daya.
A ranar Laraba, wani jami’in gwamnatin Amurka ya ce ba a ba wa Artan izinin shiga kasar ba saboda zargin “haɗin gwiwa da ake zargin ‘yan kungiyoyin ta’addanci”.
Somaliya tana daya daga cikin kasashe da dama da ke cikin jerin wadanda aka haramtawa tafiye-tafiye da Shugaba Donald Trump ya gabatar, kuma bayan ya yi magana da hukumomin Amurka, hukumar gudanarwa ta duniya Fifa ta ce Artan ba zai halarci gasar ba.
Artan ya shaida wa jaridar New York Times a wannan makon cewa jami’an kan iyaka sun yi masa tambayoyi kan alakar da ke tsakaninsa da kungiyar ‘yan ta’adda ta Somaliya Al Shabab kuma ya gaya musu cewa bai san komai game da kungiyar ba.
“Ina da cikakkun takardu da komai. Ina da takardar izinin shiga da ta dace,” in ji Artan.
“Ni kawai alkalin wasa ne wanda ke ƙoƙarin cimma burinsa, babban burin rayuwata, na zuwa gasar cin kofin duniya.”


