Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Afrika
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika

Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
Published: June 11, 2026 at 5:35 PM | By: Bala Hassan

Alkalin wasan Somalia Omar Artan, wanda aka hana shi shiga ƙasar Amurka don yin alkalancin gasar cin kofin duniya, an zabe shi domin ya jagoranci wasan cin kofin Uefa Super Cup tsakanin Paris St-Germain da Aston Villa a wannan bazarar.

An shirya fafatawar tsakanin PSG, wacce ta lashe gasar zakarun Turai a kakar wasa ta bara da Aston Villa, wacce ta yi nasara a gasar Europa League, wasan za ta gudana a ranar 12 ga Agusta a Salzburg.

A cikin wata sanarwa, hukumar kula da kwallon kafa ta Turai ta ce an yanke wannan shawara ne bayan tattaunawa da Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (Caf).

Shugaban Uefa Aleksander Ceferin ya ce: “Omar Artan ƙwararren alkalin wasa ne, wanda ya tabbatar da kansa a matakin gasa mafi girma a Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka.

“An yi ƙwallon ƙafa ne don haɗa mutane, kuma Uefa tana son nuna girmamawa ga Omar da ƙwarewarsa ta yin alkalanci, wanda hakan ya sa ya sami wannan matsayi mai daraja.

“Ina godiya ga abokina shugaban Caf Patrice Motsepe saboda goyon bayan da himma.”

Artan, wanda ya lashe kyautar alkalan wasa na maza na Caf a shekarar 2025, wm ya kasance cikin jerin alkalan wasa na duniya na Fifa tun 2018, inda ya zama dan kasar Somaliya na farko da zai yi alkalanci a gasar cin kofin duniya.

Duk da haka, jami’an kan iyaka a Miami sun ki amincewa da shi duk da cewa yana da fasfo na diflomasiyya da kuma takardar izinin shiga Amurka sau daya.

A ranar Laraba, wani jami’in gwamnatin Amurka ya ce ba a ba wa Artan izinin shiga kasar ba saboda zargin “haɗin gwiwa da ake zargin ‘yan kungiyoyin ta’addanci”.

Somaliya tana daya daga cikin kasashe da dama da ke cikin jerin wadanda aka haramtawa tafiye-tafiye da Shugaba Donald Trump ya gabatar, kuma bayan ya yi magana da hukumomin Amurka, hukumar gudanarwa ta duniya Fifa ta ce Artan ba zai halarci gasar ba.

Artan ya shaida wa jaridar New York Times a wannan makon cewa jami’an kan iyaka sun yi masa tambayoyi kan alakar da ke tsakaninsa da kungiyar ‘yan ta’adda ta Somaliya Al Shabab kuma ya gaya musu cewa bai san komai game da kungiyar ba.

“Ina da cikakkun takardu da komai. Ina da takardar izinin shiga da ta dace,” in ji Artan.

“Ni kawai alkalin wasa ne wanda ke ƙoƙarin cimma burinsa, babban burin rayuwata, na zuwa gasar cin kofin duniya.”

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola
Next Post: Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.