Hukumar Alhazai ta Kasar Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa za a fara jigilar alhazan Najeriya zuwa gida daga ranar 3 ga watan Yuni, tare da yin kira ga alhazai da su bi ka’idojin tafiye-tafiye domin kauce wa jinkiri.
Shugaban Sashen Ayyukan Jiragen Sama na hukumar, Alhaji Habib Bello, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a birnin Makkah.
Ya ce jadawalin tashin jiragen dawowa yana karkashin kamfanonin jiragen sama ne tare da amincewar Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Saudiyya (GACA), wadda ke ware lokutan tashin jirage ga kamfanoni daban-daban.
A cewar sa, kamfanin Max Air zai fara jigilar alhazan Jihar Nasarawa daga ranar 3 ga Yuni, yayin da Flynas da Air Peace za su fara jigilar alhazan jihohin Ogun da Oyo daga ranar 4 ga Yuni.
Bello ya ce an tanadi dokar daukar jakunkuna biyu masu nauyin kilo 23 kowanne da kuma jakar hannu mai nauyin kilo 8, yana mai gargadin cewa rashin bin wannan ka’ida na iya haifar da jinkirin tashi ko hana mahajjaci shiga jirgin.
Ya kuma bukaci alhazai da jami’an jihohi su sanar da hukumomi akalla sa’o’i 48 kafin ranar tafiyarsu domin saukaka shirye-shiryen fitar da fasfo, jigilar kaya da sauran muhimman matakai.
A nasa bangaren, Shugaban Kwamitin Fasfo na NAHCON a Makkah, Alhaji Abdurrahman Mohammed, ya ce an kammala matakin farko na aikin Hajjin bana cikin nasara, kuma an fara shirye-shiryen fitar da fasfofin alhazan da za su koma gida.
Ya bayyana cewa ana ajiye fasfofin alhazai ne domin kare su daga bacewa ko lalacewa, tare da tabbatar da saukin gudanar da harkokin tafiya.
Mohammed ya ce duk mahajjacin da ke shirin tafiya ya kamata ya gabatar da bayanansa akalla sa’o’i 48 kafin tashinsa domin a samu saukin fitar da fasfonsa da kuma shirya masa tafiya.
Ya tabbatar da cewa akwai matakan da aka tanada domin gano fasfofin da suka bace, yayin da za a samar da Takardar Tafiya ta Gaggawa (ETC) ga duk wanda ba a samu fasfonsa ba.
Jami’an biyu sun yi kira ga alhazai da jami’an kula da su da su ba da hadin kai domin tabbatar da cewa aikin dawo da alhazan Najeriya ya gudana cikin sauki da nasara.


