Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai
Published: June 1, 2026 at 4:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Alhazai ta Kasar Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa za a fara jigilar alhazan Najeriya zuwa gida daga ranar 3 ga watan Yuni, tare da yin kira ga alhazai da su bi ka’idojin tafiye-tafiye domin kauce wa jinkiri.

Shugaban Sashen Ayyukan Jiragen Sama na hukumar, Alhaji Habib Bello, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a birnin Makkah.

Ya ce jadawalin tashin jiragen dawowa yana karkashin kamfanonin jiragen sama ne tare da amincewar Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Saudiyya (GACA), wadda ke ware lokutan tashin jirage ga kamfanoni daban-daban.

A cewar sa, kamfanin Max Air zai fara jigilar alhazan Jihar Nasarawa daga ranar 3 ga Yuni, yayin da Flynas da Air Peace za su fara jigilar alhazan jihohin Ogun da Oyo daga ranar 4 ga Yuni.

Bello ya ce an tanadi dokar daukar jakunkuna biyu masu nauyin kilo 23 kowanne da kuma jakar hannu mai nauyin kilo 8, yana mai gargadin cewa rashin bin wannan ka’ida na iya haifar da jinkirin tashi ko hana mahajjaci shiga jirgin.

Ya kuma bukaci alhazai da jami’an jihohi su sanar da hukumomi akalla sa’o’i 48 kafin ranar tafiyarsu domin saukaka shirye-shiryen fitar da fasfo, jigilar kaya da sauran muhimman matakai.

A nasa bangaren, Shugaban Kwamitin Fasfo na NAHCON a Makkah, Alhaji Abdurrahman Mohammed, ya ce an kammala matakin farko na aikin Hajjin bana cikin nasara, kuma an fara shirye-shiryen fitar da fasfofin alhazan da za su koma gida.

Ya bayyana cewa ana ajiye fasfofin alhazai ne domin kare su daga bacewa ko lalacewa, tare da tabbatar da saukin gudanar da harkokin tafiya.

Mohammed ya ce duk mahajjacin da ke shirin tafiya ya kamata ya gabatar da bayanansa akalla sa’o’i 48 kafin tashinsa domin a samu saukin fitar da fasfonsa da kuma shirya masa tafiya.

Ya tabbatar da cewa akwai matakan da aka tanada domin gano fasfofin da suka bace, yayin da za a samar da Takardar Tafiya ta Gaggawa (ETC) ga duk wanda ba a samu fasfonsa ba.

Jami’an biyu sun yi kira ga alhazai da jami’an kula da su da su ba da hadin kai domin tabbatar da cewa aikin dawo da alhazan Najeriya ya gudana cikin sauki da nasara.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani
Next Post: Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
  • Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
  • Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
  • An Kaddamar Da Rigakafin Cutar HIV AIDS A Kasar Zimbabwe Kimiya
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.