Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa
Published: January 4, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a matsayin magajin Malam Aminu Kano wajen kishin al’umma da jajircewa kan walwalar jihar Kano.

Tinubu ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murna da ya aike wa gwamnan bisa cika shekaru 63 da haihuwa.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar Shugaba Tinubu, sauƙin kai, tawali’u da kuma jajircewar Gwamna Abba Kabir Yusuf sun bayyana karara a yadda yake tafiyar da al’amuran mulki a jihar Kano.

Shugaban ƙasar ya ƙara da cewa yana da cikakken tabbaci cewa Gwamna Yusuf yana bin sahun hangen nesa da tafarkin Malam Aminu Kano wajen jagorancin jihar, wadda ke da muhimmiyar rawa a siyasar Arewacin Najeriya.

Tinubu ya ce jajircewar gwamnan wajen kare haƙƙin talakawan birni da na karkara na daga cikin manyan dalilan da ke tabbatar da hakan.

A cewarsa, shirye-shiryen sabunta birane da gwamnatin Kano ta ɓullo da su, musamman gina gadoji da tituna masu tsawon kilomita biyar biyar a kowace ƙaramar hukuma, sun nuna ƙwazon shugabancin gwamnan.

Haka kuma, Shugaba Tinubu ya yaba da ayyana dokar ta baci da Gwamna Yusuf ya yi a ɓangaren ilimi, inda ya ce hakan ya haifar da gagarumar ci gaba, musamman yadda ɗaliban jihar Kano suka samu sakamako mai kyau a jarabawar NECO.

A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya yi wa Gwamna Abba Kabir Yusuf fatan tsawon rai da ƙarin shekaru na shugabanci masu albarka, tare da fatan ganin ƙarin ci gaba da bunƙasuwar jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari
Next Post: Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
  • Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.