Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari
Published: January 4, 2026 at 5:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƴan Agajin Izala Sun Tsallake Rijiya da Baya a Hatsarin Mota a Hanyarsu Daga Bauchi

Ƴan agajin ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah wa Iqamatis Sunnah (Izala) reshen Jihar Gombe sun tsallake rijiya da baya, bayan da motarsu ta yi hatsari a hanyar su ta dawowa daga jihar Bauchi, inda suka halarci Kamfin na ƴan agaji.

Rahotanni sun tabbatar da cewa babu asarar rai a hatsarin, sai dai wasu daga cikin su sun samu raunuka daban-daban kuma an garzaya da su zuwa asibiti domin samun kulawar gaggawa daga likitoci.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa jami’ai da masu agajin gaggawa sun kai ɗauki cikin hanzari, wanda ya taimaka matuƙa wajen rage illar da hatsarin zai iya haifarwa.

Shugabannin ƙungiyar da al’ummar yankin sun nuna godiyar su ga Allah Madaukakin Sarki bisa kare rayukan ƴan agajin, tare da yin addu’ar samun sauƙi cikin gaggawa ga waɗanda suka samu raunuka.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina
Next Post: Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa

Karin Labarai Masu Alaka

An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
  • Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.