Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina
Published: January 4, 2026 at 2:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojan Najeriya ta ce jiragen yaƙinta sun hallaka akalla ’yan bindiga 23 da ke tserewa daga jihar Kano zuwa jihar Katsina, a wani samame na haɗin gwiwa karkashin Operation Fansan Yamma.

A cewar rundunar, samamen ya biyo bayan wani hari da ake zargin ’yan bindiga sun kai a daren 1 zuwa safiyar 2 ga Janairu, 2026, a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa na Jihar Kano.

Dakarun haɗin gwiwa da ke Kano sun dakile harin cikin gaggawa tare da yi wa ’yan ta’addan mummunar ɓarna, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa jihar Katsina, Sojojin sun bi sahunsu har zuwa ƙauyen Karaɗuwa da ke Ƙaramar Hukumar Matazu.

A wata sanarwa da Mai Taimaka wa Daraktan Hulɗa da Jama’a na Birgediya na 3, Major Babatunde Zubairu, ya fitar, ya ce bayanan leƙen asiri sun nuna cewa ’yan bindigar suna gudanar da jana’izar abokansu da aka kashe a yankin Ɗan Marke, a Ƙaramar Hukumar Matazu, lokacin da dakarun sama suka ga motsinsu.

Sanarwar ta ce an ci gaba da bibiyar su har sai da suka haɗu da baburansu bayan sun ƙetare wani busasshen kwarin rafi, inda jiragen yaƙin sama suka kai musu luguden wuta.

Rundunar ta bayyana cewa an hallaka akalla ’yan ta’adda 23, yayin da ake kyautata zaton wasu da dama sun samu raunuka kuma harin ya kuma lalata makamai da kayan aiki da dama na ’yan bindigar.

Kwamandan Birgediya na 3 ya yaba da jarumtaka da jajircewar dakarun sama da na ƙasa, yana mai cewa sun nuna bajinta na musamman a fagen yaƙi.

Rundunar Soja ta tabbatar wa al’ummar jihar Kano cewa yankin na ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali, tare da ci gaba da sintiri da sa ido a kai a kai.

Ta kuma gode wa jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa a yaƙi da ’yan ta’adda, tare da kiran su da su ci gaba da samar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa jami’an tsaro wajen dakile ayyukan ta’addanci.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba
Next Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika
Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
  • Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.