Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina
Published: January 4, 2026 at 2:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojan Najeriya ta ce jiragen yaƙinta sun hallaka akalla ’yan bindiga 23 da ke tserewa daga jihar Kano zuwa jihar Katsina, a wani samame na haɗin gwiwa karkashin Operation Fansan Yamma.

A cewar rundunar, samamen ya biyo bayan wani hari da ake zargin ’yan bindiga sun kai a daren 1 zuwa safiyar 2 ga Janairu, 2026, a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa na Jihar Kano.

Dakarun haɗin gwiwa da ke Kano sun dakile harin cikin gaggawa tare da yi wa ’yan ta’addan mummunar ɓarna, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa jihar Katsina, Sojojin sun bi sahunsu har zuwa ƙauyen Karaɗuwa da ke Ƙaramar Hukumar Matazu.

A wata sanarwa da Mai Taimaka wa Daraktan Hulɗa da Jama’a na Birgediya na 3, Major Babatunde Zubairu, ya fitar, ya ce bayanan leƙen asiri sun nuna cewa ’yan bindigar suna gudanar da jana’izar abokansu da aka kashe a yankin Ɗan Marke, a Ƙaramar Hukumar Matazu, lokacin da dakarun sama suka ga motsinsu.

Sanarwar ta ce an ci gaba da bibiyar su har sai da suka haɗu da baburansu bayan sun ƙetare wani busasshen kwarin rafi, inda jiragen yaƙin sama suka kai musu luguden wuta.

Rundunar ta bayyana cewa an hallaka akalla ’yan ta’adda 23, yayin da ake kyautata zaton wasu da dama sun samu raunuka kuma harin ya kuma lalata makamai da kayan aiki da dama na ’yan bindigar.

Kwamandan Birgediya na 3 ya yaba da jarumtaka da jajircewar dakarun sama da na ƙasa, yana mai cewa sun nuna bajinta na musamman a fagen yaƙi.

Rundunar Soja ta tabbatar wa al’ummar jihar Kano cewa yankin na ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali, tare da ci gaba da sintiri da sa ido a kai a kai.

Ta kuma gode wa jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa a yaƙi da ’yan ta’adda, tare da kiran su da su ci gaba da samar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa jami’an tsaro wajen dakile ayyukan ta’addanci.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba
Next Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari

Karin Labarai Masu Alaka

Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno Tsaro
Amurka Ta Girke Jirage Marasa Matuki Tare Da Sojoji A Najeriya Afrika
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai
Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
  • Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
  • Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.