Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum
Published: December 17, 2025 at 11:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Yobe a arewa maso gabashin Najeriya ta tabbatar da samuwar wata ƙungiyar dake lalata tare da cin zarafin fursunoni a Gidan Gyaran Hali na Potiskum.

Mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdulsalam Abubakar mai ritaya, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron Majalisar Tsaron Jihar da aka gudanar a ranar Talata a Damaturu.

Abdulsalam ya bayyana lamarin a matsayin babbar cin amana, inda ya ce ana zargin wasu jami’an gidan yari da yi wa wata fursuniya ciki a cikin gidan gyaran halin.

Ya ce hakan na nuna sakaci wajen aiki da kuma rashin kulawa yadda ya kamata, yana mai cewa a ka’ida babu yadda za a yi jami’in tsaro namiji ya shiga sashen mata idan ana sa ido yadda ya dace.

Mai ba da shawarar kan tsaro ya ce, bincike na ci gaba da gudana, inda ya kara da cewa har yanzu ba a tantance adadin jami’an da ke da hannu a lamarin ba, domin ana ci gaba da kama wasu da ake zargi inda ya kara da cewa, al’amarin wata ƙungiya ce mai faɗi, bawai mutum ɗaya ba, kuma akwai masu taimaka musu ciki har da wasu jami’an mata.

Sai dai Abdulsalam ya nuna fatan cewa duk wanda aka samu da laifi a binciken da Hedikwatar Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa ke gudanarwa, za a miƙa shi ga ‘yan sanda domin gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta riga ta kai ƙorafi ga shugabancin Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa da Ma’aikatar Harkokin Cikin gida yana mai jaddada cewa gwamnati na da alhakin kare rayuka, dukiya da mutuncin al’umma.

A game da samar da tsaro lokacin bukukuwan Kirsimeti, Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, Emmanuel Ado, ya ce an shirya tsaro sosai, inda aka tura jami’ai da dama zuwa wuraren ibada da wuraren shakatawa.

Ya tabbatar wa mazauna jihar, musamman mabiya addinin Kirista, cewa za su gudanar da bukukuwansu cikin kwanciyar hankali ba tare da fargaba ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi
Next Post: Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana

Karin Labarai Masu Alaka

Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Jam’iyyar PDP Na Kara Tsunduma Cikin Mawuyacin Hali Shirye-Shirye
  • Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
  • Gwamnatin Tinubu Ta Warware Basussukan Fansho Na Shekaru 18 Afrika
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.