Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya!
Published: December 16, 2025 at 8:30 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Alh. Aliko Dangote ya jaddada wani zargi da ya shafi shugaban sashen kula da albarkatun Man Fetur na Najeriya,

Dangote, dai ya yi karin bayani da cewa Inginiya Farouk Ahmed, ya kashe dala miliyan biyu don biyawa ‘yan’yan sa kudin makarantar gaba da sakandare, inda ya kara da cewa a cikin kudin, ya kashewa dan sa

Faisal dala $210,000 don yin digiri na biyu a fannin kasuwanci a jami’ar Harvard da ke kasar Amurka.
Shugaban hadakar kamfanin Aliko Dangote, ya bayyana zargin da yake yiwa shugaban sashen kula da albarkatun man fetur na kasa (NMDPRA), Farouk Ahmed, inda ya ke zargin sa da kashe miliyoyin daloli don biyawa ‘ya’yan sa kudin makaranta a kasashen waje.

A ranar Lahadi, Alhaji Dangote ya zargi Farouk Ahmed da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, abin da yace yana kawo koma baya wajen ci gabankasar a fannoni da dama.

Yayin da yake magana a wani taro na karawa juna sani a matatar Man Dangote, Alhaji Aliko ya zargi shugabancin na NMDPRA da hada kai da ‘yan kasuwar waje, da masu shigo da Mai daga waje domin su kawo tazgaro ga matatar Mmai na cikin gida ta hanyar bayar da lasisin shigo da kayyakin Man Fetur.

Alhaji Dangote ya yi ikirarin cewa Farouk Ahmed yana wadaka da kudin da ya zarce albashin sa. Ya yi zargin cewa hudu daga cikin ‘ya’yan sa dake makarantar sakandare a kasar Switzerland, inda ake kashe musu miliyoyin daloli.

Ya ce wannan facaka abu ne da ya kamata a bincika don yana nuni da almundahana da kudin gwamnati na bangaren lura da harkokin Man Fetur.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun Alh. Aliko Dangote, a ranar Litinin, ya kara da zargin cewa, Alhaji Ahmed ya kashewa ‘ya’yan sa fiye da dala miliyan 5 a kudin makarantar sakandare a Switzerland.
Dangote ya lissafa ‘ya’yan da makarantar su, da suka hada kamar haka;

Faisal Farouk da ya yi makarantar Montreux

Farouk Jr kwalejin Aiglon

Ashraf Farouk Institute Le Rosey

Sai kuma Farhana Farouk da ta yi makarantar La Garenne International

Ya ce ko wanne daga cikin su ya yi shekara 6 a makaranta.

A cewar sa abin da aka kiyasta na kudaden makarantar sakandire da ake biya duk shekara da kudin jirgi da kudin batarwa kowanne da ya tashi kan dala $200,000 jimillar dala $4, 800,000 na yara hudu. Kwatankwacin naira Biliyan daya da miliyan dari da ashirin kudin Najeriya.

Bugu da kari, Dangote ya ce Farouk Ahmed ya kashewa yaran sa 4 dala miliyan biyu kudin makarantar gaba da sakandare, ya kara da cewa ya kashewa dan sa Faisal dala $200,000 don karo karatu a matakin digiri na biyu a harkar kasuwanci a jami’ar Harvard.

Baki daya an kashewa yara, kama daga kudin makaranta, kudin kashewa da kudin tikitin jirgi na kaiwa da komwa, jimilla kimanin dala$125,000 a kowace shekara na yara hudu kacal, idan aka hada na shekaru shekaru hudu zai kama $500,000 a tara sau hudu zai kama $2,000,000.

Faisal wanda ya kammala karatun digiri na biyu a wannan shekarar ta 2025 a jami’ara Harward da ke nan Amurka, an biya mishi $150,000 da dala $60,000 na cin abinci, tikiti da sauran makulashe kuwa suka kama dala $210, 000 a wannan shekarar kawai ta 2025.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi
Next Post: Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne

Karin Labarai Masu Alaka

An Ga Watan Ramadan A Najeriya Da Nijar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.