Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya
Published: May 25, 2026 at 12:38 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

NAHCON Ta Bukaci Mahajjata Su Sayi Dabbobin Hadaya Ta Cibiyoyin Da Aka Amince Da Su Kadai

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta yi kira ga dukkan maniyyatan Najeriya da ke gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 da su tabbatar sun sayi dabbobin Hadaya kadai ta hanyar dandalin Nusuk Masar ko kuma cibiyoyin sayarwa da Hukumar Kula da Ayyukan Hadaya da Adahi ta Masarautar Saudiyya ta amince da su.

Hukumar ta jaddada cewa bai kamata mahajjata su yi hulɗa da mutane ko ƙungiyoyi da ba su da izini ba wajen saye, talla, ko gudanar da duk wani aiki da ya shafi Hadaya da Adahi.

NAHCON ta bayyana cewa wannan mataki an ɗauke shi ne domin kare mahajjata daga zamba, damfara da sauran hanyoyin cutarwa, tare da tabbatar da cewa an kiyaye haƙƙoƙinsu a lokacin gudanar da ibadun Hajji.

Hukumar ta kuma bukaci mahajjata su yi amfani da hanyoyin da aka amince da su kawai domin tabbatar da cewa an gudanar da ibadar Hadaya da Adahi yadda Shari’ar Musulunci ta tanada tare da bin dokoki da ƙa’idojin Masarautar Saudiyya.

Hakazalika, an umarci Hukumomi da Hukumar Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, Hukumomin Hajji da Umrah, Kwamitocin Alhazai da kuma Kamfanonin Shirya Hajji (Tour Operators) da su wayar da kan mahajjata tare da tabbatar da cikakken bin wannan umarni.

NAHCON ta yi addu’ar Allah Ya karɓi ibadun mahajjata baki ɗaya, Ya ba su Hajji Mabrur, Ya kuma dawo da su gida lafiya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11
Next Post: Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki Labarai
Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
Yusuf Gawuna Ya Koma Jam’iyar ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Yace Kawayen Amurka A Kungiyar NATO Basa Goyon Bayan Su Afrika
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
  • Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
  • Jam’iyyar PDP Na Kara Tsunduma Cikin Mawuyacin Hali Shirye-Shirye
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.