Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda
Published: May 22, 2026 at 2:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC a jihar Kano dake Najeriya ta tabbatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar domin zaɓen shekarar 2027 ba tare da hamayya ba.

An gudanar da taron tabbatar da ɗan takarar ne a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, inda dubban magoya baya da shugabannin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar suka halarta duk da ruwan sama da aka yi a lokacin taron.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin ne ya gabatar da kudirin amincewa da Gwamna Yusuf a matsayin zaɓin bai ɗaya na jam’iyyar APC a Kano. Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdurrahman Kawu Sumaila ya mara wa kudirin baya, yana mai bayyana cewa jam’iyyar ta haɗa kai wajen mara wa gwamnan baya domin sake neman wa’adin mulki na biyu.

Shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na APC, Muntari Shagari, ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika dukkan sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma dokokin zaɓe, saboda haka aka tabbatar da shi a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna na APC a Kano domin zaɓen shekarar 2027.

A jawabinsa bayan tabbatar da shi, Gwamna Yusuf ya gode wa wakilan jam’iyyar da shugabanni bisa irin goyon baya da amincewar da suka nuna masa. Ya ce zai ci gaba da aiwatar da manufofin raya jihar Kano musamman a fannoni kamar ilimi, lafiya, noma, samar wa matasa ayyukan yi da kuma bunƙasa ababen more rayuwa.

Hakazalika, gwamnan ya bayyana goyon bayansa ga sake zaɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa
Next Post: Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika
Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Afrika
  • Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.