Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda
Published: May 22, 2026 at 2:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC a jihar Kano dake Najeriya ta tabbatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar domin zaɓen shekarar 2027 ba tare da hamayya ba.

An gudanar da taron tabbatar da ɗan takarar ne a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, inda dubban magoya baya da shugabannin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar suka halarta duk da ruwan sama da aka yi a lokacin taron.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin ne ya gabatar da kudirin amincewa da Gwamna Yusuf a matsayin zaɓin bai ɗaya na jam’iyyar APC a Kano. Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdurrahman Kawu Sumaila ya mara wa kudirin baya, yana mai bayyana cewa jam’iyyar ta haɗa kai wajen mara wa gwamnan baya domin sake neman wa’adin mulki na biyu.

Shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na APC, Muntari Shagari, ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika dukkan sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma dokokin zaɓe, saboda haka aka tabbatar da shi a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna na APC a Kano domin zaɓen shekarar 2027.

A jawabinsa bayan tabbatar da shi, Gwamna Yusuf ya gode wa wakilan jam’iyyar da shugabanni bisa irin goyon baya da amincewar da suka nuna masa. Ya ce zai ci gaba da aiwatar da manufofin raya jihar Kano musamman a fannoni kamar ilimi, lafiya, noma, samar wa matasa ayyukan yi da kuma bunƙasa ababen more rayuwa.

Hakazalika, gwamnan ya bayyana goyon bayansa ga sake zaɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa
Next Post: Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai
Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • NDPHC Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Gombe Wajen Inganta Wutar Lantarki Afrika
  • Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.