Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda
Published: May 22, 2026 at 2:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC a jihar Kano dake Najeriya ta tabbatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar domin zaɓen shekarar 2027 ba tare da hamayya ba.

An gudanar da taron tabbatar da ɗan takarar ne a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, inda dubban magoya baya da shugabannin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar suka halarta duk da ruwan sama da aka yi a lokacin taron.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin ne ya gabatar da kudirin amincewa da Gwamna Yusuf a matsayin zaɓin bai ɗaya na jam’iyyar APC a Kano. Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdurrahman Kawu Sumaila ya mara wa kudirin baya, yana mai bayyana cewa jam’iyyar ta haɗa kai wajen mara wa gwamnan baya domin sake neman wa’adin mulki na biyu.

Shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na APC, Muntari Shagari, ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika dukkan sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma dokokin zaɓe, saboda haka aka tabbatar da shi a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna na APC a Kano domin zaɓen shekarar 2027.

A jawabinsa bayan tabbatar da shi, Gwamna Yusuf ya gode wa wakilan jam’iyyar da shugabanni bisa irin goyon baya da amincewar da suka nuna masa. Ya ce zai ci gaba da aiwatar da manufofin raya jihar Kano musamman a fannoni kamar ilimi, lafiya, noma, samar wa matasa ayyukan yi da kuma bunƙasa ababen more rayuwa.

Hakazalika, gwamnan ya bayyana goyon bayansa ga sake zaɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa
Next Post: Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani

Karin Labarai Masu Alaka

Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
  • Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
  • Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika
  • Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.