Jam’iyyar APC a jihar Kano dake Najeriya ta tabbatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar domin zaɓen shekarar 2027 ba tare da hamayya ba.
An gudanar da taron tabbatar da ɗan takarar ne a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, inda dubban magoya baya da shugabannin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar suka halarta duk da ruwan sama da aka yi a lokacin taron.
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin ne ya gabatar da kudirin amincewa da Gwamna Yusuf a matsayin zaɓin bai ɗaya na jam’iyyar APC a Kano. Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdurrahman Kawu Sumaila ya mara wa kudirin baya, yana mai bayyana cewa jam’iyyar ta haɗa kai wajen mara wa gwamnan baya domin sake neman wa’adin mulki na biyu.
Shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na APC, Muntari Shagari, ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika dukkan sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma dokokin zaɓe, saboda haka aka tabbatar da shi a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna na APC a Kano domin zaɓen shekarar 2027.
A jawabinsa bayan tabbatar da shi, Gwamna Yusuf ya gode wa wakilan jam’iyyar da shugabanni bisa irin goyon baya da amincewar da suka nuna masa. Ya ce zai ci gaba da aiwatar da manufofin raya jihar Kano musamman a fannoni kamar ilimi, lafiya, noma, samar wa matasa ayyukan yi da kuma bunƙasa ababen more rayuwa.
Hakazalika, gwamnan ya bayyana goyon bayansa ga sake zaɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027.


