Fadar Shugaban Kasar Najeriya ta karyata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya sunan Najeriya zuwa “United States of Nigeria” tare da soke dokar Shari’a a Arewacin kasar.
A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar 21 ga watan Mayun 2026, gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin “labarin karya” da wasu ke yadawa domin haddasa rikici da tayar da hankalin jama’a gabanin babban zaben 2027.
Sanarwar ta ce babu wani kudiri da Shugaba Tinubu ke shirin aikewa Majalisar Dokoki ta Kasa mai suna “Project True Federation” kamar yadda ake yadawa.
Fadar shugaban kasar ta zargi masu yada rahoton da kokarin haifar da rabuwar kai da rikicin siyasa a kasar.
“’Yan Najeriya su yi watsi gaba daya da wannan labari saboda masu yada shi makiyan zaman lafiya ne kuma masu neman tayar da tarzoma,” in ji sanarwar.
Gwamnatin ta kuma bayyana cewa sauya kundin tsarin mulkin kasa ba abu ne da shugaban kasa ko majalisa za su yi kai tsaye ba, domin akwai matakai masu tsauri da suka hada da samun amincewar kashi biyu bisa uku na majalisun dokokin kasar da kuma majalisun dokokin jihohi 24.
Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu na mayar da hankali ne wajen aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki da gwamnatin sa ta fara domin inganta rayuwar ’yan Najeriya.
Fadar shugaban kasar ta gargadi jama’a da su rika taka-tsantsan wajen karanta da yada rahotannin karya musamman yayin da harkokin yakin neman zabe ke kara karatowa.


