Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya.
Published: December 4, 2025 at 11:40 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 5, 2025

Kyaftin din Super Eagles William Troost-Ekong ya sanar da yin ritaya daga buga kwallon kafa na kasa da kasa.

Hakan yasa dan wasan mai shekaru 32 ba zai buga gasar cin kofin kasashen Afirka da ke tafe ba, wanda hakan shine ya kasance babban gasa ta farko da Najeriya za ta halarta ba tare da shi ba cikin kusan shekaru 10.

Troost-Ekong, wanda ya yi wasanni 83 kuma ya buga manyan gasa biyar, ya ce wannan shawarar ta zo ne da cikin kwanciyar hankali da sanin cewa a duk wadannan muhimman abubuwan da na yi na bayar da duk wata gudumawa da nake da shi.”

Da yake tunani game da tafiyarsa, ya ce sanya rigar babban kungiyar kwallon kafar Najeriya “ya fi buga kwallon kafa.

Tsohon kyaftin din Super Eagles ya bayyana wasansa na farko a shekarar 2015 a matsayin lokacin da komai ya canza, yana tunawa da yadda marigayi Stephen Keshi ya amince da shi tun da farko “in ji shi.

Troost-Ekong ya nuna jin dadi na damar da ya samu na jagorantar Najeriya, musamman a lokacin gasar AFCON ta 2023, inda aka nada shi Dan wasan Gasar bayan ya zura kwallo a wasan karshe.

“Wannan gasar ta koya min abin da ake nufi da zama dan Najeriya: muna fafatawa cikin wahala kuma muna kokari,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa magoya baya da abokan wasansa wadanda suka tafiya tare ta tsawon shekaru goma.

An haife William a ƙasar Netherlands mahaifiyarsa ‘yar kasar Holland mahaifinsa dan Najeriya, maisuna Troost-Ekong ya wakilci Netherlands a matakin matasa kafin daga bisani ya sadaukar da kansa ga Najeriya.

Ya fara buga wasa a matakin farko a watan Yunin 2015 a wasan share fagen shiga gasar AFCON da Chad.

Kwallaye biyar da ya ci a gasar cin kofin kasashen Afirka sun kasance mafi yawan jimillar kwallaye da wani mai tsaron baya ya ci a tarihin gasar.

Troost-Ekong ya buga wasanin kwallon kafa a kasashen Turai, inda ya yi wasa a Ingila, Italiya, Turkiyya da Girka kafin ya koma PAOK a watan Yulin 2023.

A watan Agustan 2024, ya koma ƙungiyar Al-Kholood ta Saudiyya.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel
Next Post: Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto

Karin Labarai Masu Alaka

CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026 Wasanni
Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028 Wasanni
Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata Afrika
  • Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa Afrika
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.