Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya.
Published: December 4, 2025 at 11:40 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 5, 2025

Kyaftin din Super Eagles William Troost-Ekong ya sanar da yin ritaya daga buga kwallon kafa na kasa da kasa.

Hakan yasa dan wasan mai shekaru 32 ba zai buga gasar cin kofin kasashen Afirka da ke tafe ba, wanda hakan shine ya kasance babban gasa ta farko da Najeriya za ta halarta ba tare da shi ba cikin kusan shekaru 10.

Troost-Ekong, wanda ya yi wasanni 83 kuma ya buga manyan gasa biyar, ya ce wannan shawarar ta zo ne da cikin kwanciyar hankali da sanin cewa a duk wadannan muhimman abubuwan da na yi na bayar da duk wata gudumawa da nake da shi.”

Da yake tunani game da tafiyarsa, ya ce sanya rigar babban kungiyar kwallon kafar Najeriya “ya fi buga kwallon kafa.

Tsohon kyaftin din Super Eagles ya bayyana wasansa na farko a shekarar 2015 a matsayin lokacin da komai ya canza, yana tunawa da yadda marigayi Stephen Keshi ya amince da shi tun da farko “in ji shi.

Troost-Ekong ya nuna jin dadi na damar da ya samu na jagorantar Najeriya, musamman a lokacin gasar AFCON ta 2023, inda aka nada shi Dan wasan Gasar bayan ya zura kwallo a wasan karshe.

“Wannan gasar ta koya min abin da ake nufi da zama dan Najeriya: muna fafatawa cikin wahala kuma muna kokari,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa magoya baya da abokan wasansa wadanda suka tafiya tare ta tsawon shekaru goma.

An haife William a ƙasar Netherlands mahaifiyarsa ‘yar kasar Holland mahaifinsa dan Najeriya, maisuna Troost-Ekong ya wakilci Netherlands a matakin matasa kafin daga bisani ya sadaukar da kansa ga Najeriya.

Ya fara buga wasa a matakin farko a watan Yunin 2015 a wasan share fagen shiga gasar AFCON da Chad.

Kwallaye biyar da ya ci a gasar cin kofin kasashen Afirka sun kasance mafi yawan jimillar kwallaye da wani mai tsaron baya ya ci a tarihin gasar.

Troost-Ekong ya buga wasanin kwallon kafa a kasashen Turai, inda ya yi wasa a Ingila, Italiya, Turkiyya da Girka kafin ya koma PAOK a watan Yulin 2023.

A watan Agustan 2024, ya koma ƙungiyar Al-Kholood ta Saudiyya.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel
Next Post: Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto

Karin Labarai Masu Alaka

Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu Afrika
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
  • Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.