Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
Published: January 14, 2026 at 8:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya da ASUU sun kulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo karshen yawan yajin aiki a jami’o’in Najeriya

A wani muhimmin mataki da ake ganin zai sauya fasalin ilimin jami’a a Najeriya, Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) sun kulla wata babbar yarjejeniya da nufin inganta jin daɗin malamai, tabbatar da zaman lafiyar aiki da kuma kawo ƙarshen yawan yajin aikin da ya shafe shekaru yana durƙusar da jami’o’in ƙasar.

An bayyana yarjejeniyar ta shekarar 2025 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU a ranar Laraba a Abuja, inda Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana ta a matsayin wani sabon shafi a tarihin ilimin gaba da sakandare a Najeriya.

A cewarsa, yarjejeniyar ba rubutun takarda bane kawai, illa alamar dawo da amana, girmamawa da kwarin gwiwa ga tsarin jami’o’in ƙasar bayan shekaru na rashin tabbas da yajin aiki.

Ministan ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa daukar mataki na musamman wajen fuskantar matsalar da ta dade tana addabar jami’o’i, tana lalata jadawalin karatu tare da rusa makomar dalibai miliyoyi.

“Wannan ne karon farko da Shugaban Ƙasa mai ci ya tsaya tsayin daka wajen fuskantar wannan ƙalubale kai tsaye, ya ba matsalar kulawar shugabancin da ta dace,” in ji Alausa, yana mai cewa gwamnatin ta zaɓi tattaunawa maimakon rikici, gyara maimakon jinkiri, da warware matsala maimakon surutu.

Daya daga cikin manyan abubuwan da yarjejeniyar ta ƙunsa shi ne ƙarin albashin malaman jami’a da kashi 40 cikin 100, wanda Hukumar Albashi, Kuɗaɗen Shiga da Albashi ta Ƙasa (NSIWC) ta amince da shi Sabon tsarin albashin zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

A karkashin sabon tsarin, albashin malaman zai haɗa da CONUASS da kuma ingantaccen alawus na kayan aikin koyarwa da bincike (CATA). An ƙarfafa CATA domin tallafa wa wallafa mujallu, halartar taruka, amfani da intanet, rajistar ƙungiyoyin ƙwararru da rubuce-rubucen littattafai, domin ƙara gogayya da rage guduwar ƙwararru zuwa ƙasashen waje.

Haka kuma, yarjejeniyar ta sake tsara alawus-alawus guda tara na Earned Academic Allowances, inda aka fayyace su sarai tare da danganta su kai tsaye da ayyukan da ake yi kamar kula da daliban digirin digirgir, aikin asibiti, jarrabawa da shugabancin harkokin ilimi.

A wani sabon salo da ba a taba gani ba a tsarin jami’o’in Najeriya, Gwamnatin Tarayya ta amince da wani alawus na musamman ga manyan malaman jami’a, wato Farfesoshi da Masu Karatu (Readers).

A karkashin wannan tsari, Farfesoshi za su rika karɓar naira miliyan 1.74 a shekara (naira 140,000 a wata), yayin da Readers za su karɓi naira 840,000 a shekara (naira 70,000 a wata).

Ministan ya ce an samar da wannan alawus ne domin ƙarfafa bincike, tsara takardu da inganta gudanarwa, ta yadda manyan malamai za su fi mayar da hankali kan koyarwa, renon matasa da kirkire-kirkire.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata a karkashin shirin Renewed Hope Agenda, tare da ci gaba da tattaunawa da gyare-gyare a fannin ilimi.

Masu ruwa da tsaki na ganin yarjejeniyar za ta kawo sabon zamani na kwanciyar hankali da inganci a jami’o’in Najeriya, tare da dawo da daidaito a jadawalin karatu da kuma sabunta fata ga dalibai da iyaye.

Ministan ya yabawa tawagogin tattaunawar bangarorin biyu, karkashin jagorancin Alhaji Yayale Ahmed daga bangaren Gwamnatin Tarayya da Farfesa Pius Piwuna daga ASUU, tare da tsohon shugabancin ASUU na Farfesa Emmanuel Osodeke, bisa rawar da suka taka wajen samar da wannan nasara.

A karshe, Alausa ya ce tarihi ba zai tuna wannan rana a matsayin ranar kaddamar da yarjejeniya kawai ba, illa ranar da Najeriya ta zabi tattaunawa, gaskiya da jajircewar shugabanci a matsayin hanyar warware matsalolin da suka dade suna addabar kasa.

Da yarjejeniyar ta kammala, al’ummar Najeriya na fatan cewa zamanin rufe jami’o’i na dogon lokaci zai zama tarihi, yayin da ake sa ran samun kwanciyar hankali, ƙwarewa da gogayya da jami’o’in duniya a fannin ilimi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
Next Post: Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
  • Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.