Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34
Published: December 29, 2025 at 4:42 PM | By: Bala Hassan

Sojoji sun hallaka ‘yan ta’adda sama da 80, sun ceto mutane 34 a jihohi da dama

Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya ta sanar da cewa dakarunta sun hallaka ‘yan ta’adda sama da 80, tare da ceto mutane 34 da aka sace, a jerin hare-haren haɗin gwiwa da aka gudanar tsakanin ranakun 25 zuwa 29 ga Disamba, 2025.

Wata majiya mai tushe daga Hedkwatar Sojin Ƙasa ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa an samu waɗannan nasarori ne a jihohin Borno, Adamawa, Sokoto, Katsina, Neja, Zamfara, Filato, Delta, Cross River da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja (FCT).

A jihar Borno, majiyar ta ce hare-haren sama tare da bin diddigi na ƙasa da aka kai a Sowolwolo, cikin Ƙaramar Hukumar Bama, da kewayenta, sun yi sanadin hallaka ‘yan ta’adda 19, tare da rusa sansanonin ajiyar kayayyakin su da tarwatsa hanyoyin sadarwar ISWAP da JAS.

Ta ƙara da cewa wasu hare-hare na gaba da aka kai a yankunan Gulumba Gana, Kumshe, Kasho Miri da Chongolokura sun yi sanadin hallaka ƙarin ‘yan ta’adda 38. Haka kuma, bayanan leƙen asiri da sa ido (ISR) sun gano manyan shugabannin ‘yan ta’adda da ake shirin kai musu hari nan gaba.

A jihohin Neja da Katsina kuwa, majiyar ta bayyana cewa dakarun soji sun fatattaki hare-haren ‘yan ta’adda da aka kai sansanin FOB Kwanar Dutse a Ƙaramar Hukumar Mariga, da kuma kan hanyar Shanono–Katsina. A yayin wannan samame, an ceto farar hula guda ɗaya tare da ƙwato shanu 78 da tumaki 28 da ‘yan ta’addan suka sace.

Game da ayyukan ceto daga hannun masu garkuwa da mutane, majiyar ta ce a jihar Kebbi, dakarun Bataliya ta 223 sun ceto mutane 16 bayan samun bayanan sirri a ƙauyen Unashi da ke Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu.

A jihar Filato kuma, an ceto mutum guda a yankin Yaka Naji Jandutse da ke Ƙaramar Hukumar Wase.

Majiyar ta ƙara da cewa dakarun sun kuma dakile ayyukan ta’addanci da laifuka a sassa daban-daban na ƙasar, inda suka cafke masu haƙar ma’adinan zinare ba bisa ƙa’ida ba guda 11 a birnin Tarayya Abuja. Haka kuma, an kama wasu mutane biyu da ake zargi da fashi da makami a Filato, tare da kwato kuɗaɗen da suka sace.

A jihar Delta, an cafke masu satar ɗanyen mai guda biyu, inda aka ƙwato jarkoki 104 (lita 2,600) na ɗanyen mai. A Cross River kuwa, an kama wasu da ake zargin ‘yan fashin teku nr mutum uku da ke da alaƙa da ƙungiyar ‘yan bindiga ta BIG JOE.

Majiyar ta jaddada cewa waɗannan ayyuka na nuna ƙudirin sojojin Najeriya na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tabbatar da bin doka da oda, da kuma wanzar da zaman lafiya da tsaro a dukkan yankunan da abin ya shafa.

Ta kuma sake tabbatar da aniyar Rundunar Sojin Ƙasa ta ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro bisa sahihan bayanan sirri, ceto waɗanda aka sace, da kuma murƙushe duk wata barazana daga ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka a faɗin ƙasar.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun
Next Post: Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe

Karin Labarai Masu Alaka

An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki Afrika
Atiku: Zaben 2027 Zai Zamo Karo Na Karshe Da Zan Nemi Shugabancin Najeriya Afrika
Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan Labarai
  • Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
  • Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
  • Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
  • Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci Afrika
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
  • Bassirou: Tawagar Senegal Zasu Samu Kyautar Kudi Da Filaye Sakamakon Nasarar Da sukayi AFCON 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.