Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Published: December 24, 2025 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban hafsan hafsoshin sojan kasar Libya, Mohammed Ali Ahmed al-Haddad, ya mutu a lokacin da jirgin saman da yake ciki yayi hatsari bayan tashin sa daga Ankara, babban birnin Turkiyya ranar talata da maraice.

Fira ministan gwamnatin kasar Libya wadda kasashen duniya suka amince da ita, Abdulhamid Dbeibah, ya fada cikin wata sanarwa cewa akwai wasu jami’an gwamnatin ta Libya su hudu a cikin wannan jirgi.

Fira ministan yace wannan lamari ya faru ne a lokacin da babban hafsan tare da tawagarsa suke komawa gida a bayan ziyarar aiki a babban birnin na Turkiyya.

Yace sauran wadanda suke cikin wannan jirgi sun hada da kwamandan rundunar sojojin kasar ta Libya, da daraktan hukumar kere-keren kayan soja, da wani mai bawa babban hafsan shawara tare da wani mai daukar hoto daga ofishinsa.

Ministan harkokin cikin gidan Turkiyya, Ali Yerlikaya ya fada a shafin sada zumunci na X cewa jirgin ya tashi a kan hanyar komawa Tripoli daga filin jirgin saman Esenboga na Ankara da karfe 5 da minti 10 na yamma agogon kasar, kuma ya bace da karfe 5 da minti 52. Ya ce hukumomi sun gano inda jirgin ya fadi a gundumar Haymana ta lardin Ankara.

Yace wannan jirgi kirar Dassault Falcon-50, ya nemi a ba shi iznin saukar gaggawa a lokacin da yake wucewa ta samaniyar Haymana, amma sai aka kasa samunsa ta rediyo.

Ba a san abinda ya haddasa faduwar jirgin ba, amma Ministan shari’a na Turkiyya, Yilmaz Tunc, yace an kaddamar da bincike.

Wani karamin ministan harkokin siyasa da sadarwa a gwamnatin hadin kan kasa ta Libya, Walid Ellafi, ya fadawa kafar sadarwar Al-Ahrar ta libya cewa jirgin na haya ne daga wani kamfani a kasar Malta sannan yace jami’ai ba su da cikakken bayani a game da tarihin wannan jirgi ko wanda ya mallake shi, amma dai abu ne da zai fito a binciken da aka kaddamar.

Gwamnatin kasar wadda ita ce kadai MDD ta amince da ita a zaman hukuma a kasar libya, ta ayyana zaman makoki na kwanaki uku a kasar.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Next Post: Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
Jihar Filato Ta Rufe Makarantu Don Dakile Yaduwar Diphtheria Afrika
Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
  • Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.