Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Published: December 24, 2025 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban hafsan hafsoshin sojan kasar Libya, Mohammed Ali Ahmed al-Haddad, ya mutu a lokacin da jirgin saman da yake ciki yayi hatsari bayan tashin sa daga Ankara, babban birnin Turkiyya ranar talata da maraice.

Fira ministan gwamnatin kasar Libya wadda kasashen duniya suka amince da ita, Abdulhamid Dbeibah, ya fada cikin wata sanarwa cewa akwai wasu jami’an gwamnatin ta Libya su hudu a cikin wannan jirgi.

Fira ministan yace wannan lamari ya faru ne a lokacin da babban hafsan tare da tawagarsa suke komawa gida a bayan ziyarar aiki a babban birnin na Turkiyya.

Yace sauran wadanda suke cikin wannan jirgi sun hada da kwamandan rundunar sojojin kasar ta Libya, da daraktan hukumar kere-keren kayan soja, da wani mai bawa babban hafsan shawara tare da wani mai daukar hoto daga ofishinsa.

Ministan harkokin cikin gidan Turkiyya, Ali Yerlikaya ya fada a shafin sada zumunci na X cewa jirgin ya tashi a kan hanyar komawa Tripoli daga filin jirgin saman Esenboga na Ankara da karfe 5 da minti 10 na yamma agogon kasar, kuma ya bace da karfe 5 da minti 52. Ya ce hukumomi sun gano inda jirgin ya fadi a gundumar Haymana ta lardin Ankara.

Yace wannan jirgi kirar Dassault Falcon-50, ya nemi a ba shi iznin saukar gaggawa a lokacin da yake wucewa ta samaniyar Haymana, amma sai aka kasa samunsa ta rediyo.

Ba a san abinda ya haddasa faduwar jirgin ba, amma Ministan shari’a na Turkiyya, Yilmaz Tunc, yace an kaddamar da bincike.

Wani karamin ministan harkokin siyasa da sadarwa a gwamnatin hadin kan kasa ta Libya, Walid Ellafi, ya fadawa kafar sadarwar Al-Ahrar ta libya cewa jirgin na haya ne daga wani kamfani a kasar Malta sannan yace jami’ai ba su da cikakken bayani a game da tarihin wannan jirgi ko wanda ya mallake shi, amma dai abu ne da zai fito a binciken da aka kaddamar.

Gwamnatin kasar wadda ita ce kadai MDD ta amince da ita a zaman hukuma a kasar libya, ta ayyana zaman makoki na kwanaki uku a kasar.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Next Post: Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
  • Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
  • Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.