Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Published: December 24, 2025 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban hafsan hafsoshin sojan kasar Libya, Mohammed Ali Ahmed al-Haddad, ya mutu a lokacin da jirgin saman da yake ciki yayi hatsari bayan tashin sa daga Ankara, babban birnin Turkiyya ranar talata da maraice.

Fira ministan gwamnatin kasar Libya wadda kasashen duniya suka amince da ita, Abdulhamid Dbeibah, ya fada cikin wata sanarwa cewa akwai wasu jami’an gwamnatin ta Libya su hudu a cikin wannan jirgi.

Fira ministan yace wannan lamari ya faru ne a lokacin da babban hafsan tare da tawagarsa suke komawa gida a bayan ziyarar aiki a babban birnin na Turkiyya.

Yace sauran wadanda suke cikin wannan jirgi sun hada da kwamandan rundunar sojojin kasar ta Libya, da daraktan hukumar kere-keren kayan soja, da wani mai bawa babban hafsan shawara tare da wani mai daukar hoto daga ofishinsa.

Ministan harkokin cikin gidan Turkiyya, Ali Yerlikaya ya fada a shafin sada zumunci na X cewa jirgin ya tashi a kan hanyar komawa Tripoli daga filin jirgin saman Esenboga na Ankara da karfe 5 da minti 10 na yamma agogon kasar, kuma ya bace da karfe 5 da minti 52. Ya ce hukumomi sun gano inda jirgin ya fadi a gundumar Haymana ta lardin Ankara.

Yace wannan jirgi kirar Dassault Falcon-50, ya nemi a ba shi iznin saukar gaggawa a lokacin da yake wucewa ta samaniyar Haymana, amma sai aka kasa samunsa ta rediyo.

Ba a san abinda ya haddasa faduwar jirgin ba, amma Ministan shari’a na Turkiyya, Yilmaz Tunc, yace an kaddamar da bincike.

Wani karamin ministan harkokin siyasa da sadarwa a gwamnatin hadin kan kasa ta Libya, Walid Ellafi, ya fadawa kafar sadarwar Al-Ahrar ta libya cewa jirgin na haya ne daga wani kamfani a kasar Malta sannan yace jami’ai ba su da cikakken bayani a game da tarihin wannan jirgi ko wanda ya mallake shi, amma dai abu ne da zai fito a binciken da aka kaddamar.

Gwamnatin kasar wadda ita ce kadai MDD ta amince da ita a zaman hukuma a kasar libya, ta ayyana zaman makoki na kwanaki uku a kasar.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Next Post: Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta

Karin Labarai Masu Alaka

Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
Jam’iyyar APC Ta Ayana Jamilu Gwamna A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Gombe Afrika
An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
  • Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
  • Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.