Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta
Published: December 24, 2025 at 10:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel yace tilas a biyo bayan kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen da kaddamar da gagarumin farmaki a kan ‘yan ta’adda cikin ‘yan kwanakin da suke tafe a yankin da ta’addanci yayi tsanani.

Shugaban Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore, bayyi karin bayani akan wannan furuci nasa ba, a bayan da aka ayyana shi a zaman shugaban Kungiyar Kawancen Kasashen Yankin Sahel, kungiyar da kasashe 3 dake cikinta suka balle daga cikin kungiyar Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, ko CDEAO, a wannan shekarar.

Kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar sun fi fuskantar ta’addanci a yankin bakin iyakokinsu a yayin da wannan yanki na Sahel dake kudu da hamadar Sahara ya zamo inda aka fi ganin ayyukan ‘yan ta’adda masu alaka da al Qaida da kungiyar Daesh, watau ISIS.

Shugabannin kasashen uku sun cimma daidaituwa a taron kolinsu na ranar talata, a kan bunkasa hadin kan tsaro da na tattalin arziki, kuma a karshen makon nan, kasashen uku sun kaddanar da sabuwar bataliya ta hadin guiwa wadda zata yaki ‘yan ta’adda na yankin sannan ana sa ran zata kumshi dakaru dubu 5.

Shugaban Jamhuriyar Nijar, Abdourahamane Tchiani, yace kungiyarsu ta samu nasarar kawo karshen sojojin mamaya a cikin kasashensu, bisa dukkan alamu gugar zana yake yi kan shawarar da kasashen suka yanke na korar sojojin faransa da Amurka daga cikin kasashensu.

Tchiani ya kara da cewa babu wata kasa ko kungiya da a yanzu zata gaya musu abinda ya kamata su yi.

Yanzu dai kasashen uku, sun karkata ga kasare Rasha domin tallafa musu wajen ayyukan tsaron yankinsu.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Next Post: Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
  • Hukumar ICPC Ta Kwato Makudan Kudade Rediyo
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.