Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji
Published: December 10, 2025 at 10:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon shugaban Hukumar Karɓar Korafe-korafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya zargi tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da hannu a kama shi da jami’an rundunar ‘yansandan Najeriya tayi a ranar Juma’a.

An kama Magaji ne a ofishinsa da ke Kano ta hannun wasu jami’an ‘yan sanda inda suka shaida masa cewa suna aiki ne da umarnin Sufeto Janar na ‘Yansanda.

Da yake zantawa da Manema labarai jim kaɗan bayan sakin sa a ranar Asabar, tsohon shugaban PCACC ya ce matsalarsa ta samo asali ne daga wasu korafe korafe da Ganduje da tsohon Manajan Daraktan Hukumar KASCO ta Jihar Kano, Bala Inuwa, suka shigar.

A cewarsa, Ganduje ya zarge shi da “ batanci” da suka shafi takaddamar shari’a da ake yi kan mallakar hannun jarin Gwamnatin Jihar Kano a kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

“Kun sani, tun da na bar kujerar shugaban PCACC, na koma aikin lauya gaba ɗaya, kuma ni ne babban lauya a shari’ar Dala Inland Dry Port,” in ji shi.

Ya bayyana cewa bayan kama shi, kai tsaye aka wuce da shi Abuja cikin tsauraran matakan tsaro.

“An kama ni, an tsare ni tsakanin jami’an ‘yan sanda zuwa Abuja, jami’ai biyu dauke da bindigogi a gefena, sannan wasu uku a kujerar gaba, aka tashi da ni daga Kano zuwa Abuja.

“Muka yi tafiya cikin dare har muka isa wajen ƙarfe 3:00 na asuba,” in ji shi.

Muhyi Magaji ya ƙara da cewa duk da ya dage yana neman a nuna masa takardar kama shi, jami’an sun ƙi nuna masa, suna cewa a Abuja za a gabatar masa.

Ya bayyana cewa an bayar da belinsa, sai dai an umarce shi da ya koma Abuja ranar Laraba tare da mika fasfon sa na fita ƙasashen waje.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade
Next Post: EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
NANPAN Ta Wayar Da Al’umma Kan Amfanin Shayar Da Jarirai Nono Kaɗai Afrika
Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Daƙile Yaɗuwar Makamai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Afrika
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.