Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji
Published: December 10, 2025 at 10:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon shugaban Hukumar Karɓar Korafe-korafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya zargi tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da hannu a kama shi da jami’an rundunar ‘yansandan Najeriya tayi a ranar Juma’a.

An kama Magaji ne a ofishinsa da ke Kano ta hannun wasu jami’an ‘yan sanda inda suka shaida masa cewa suna aiki ne da umarnin Sufeto Janar na ‘Yansanda.

Da yake zantawa da Manema labarai jim kaɗan bayan sakin sa a ranar Asabar, tsohon shugaban PCACC ya ce matsalarsa ta samo asali ne daga wasu korafe korafe da Ganduje da tsohon Manajan Daraktan Hukumar KASCO ta Jihar Kano, Bala Inuwa, suka shigar.

A cewarsa, Ganduje ya zarge shi da “ batanci” da suka shafi takaddamar shari’a da ake yi kan mallakar hannun jarin Gwamnatin Jihar Kano a kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

“Kun sani, tun da na bar kujerar shugaban PCACC, na koma aikin lauya gaba ɗaya, kuma ni ne babban lauya a shari’ar Dala Inland Dry Port,” in ji shi.

Ya bayyana cewa bayan kama shi, kai tsaye aka wuce da shi Abuja cikin tsauraran matakan tsaro.

“An kama ni, an tsare ni tsakanin jami’an ‘yan sanda zuwa Abuja, jami’ai biyu dauke da bindigogi a gefena, sannan wasu uku a kujerar gaba, aka tashi da ni daga Kano zuwa Abuja.

“Muka yi tafiya cikin dare har muka isa wajen ƙarfe 3:00 na asuba,” in ji shi.

Muhyi Magaji ya ƙara da cewa duk da ya dage yana neman a nuna masa takardar kama shi, jami’an sun ƙi nuna masa, suna cewa a Abuja za a gabatar masa.

Ya bayyana cewa an bayar da belinsa, sai dai an umarce shi da ya koma Abuja ranar Laraba tare da mika fasfon sa na fita ƙasashen waje.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade
Next Post: EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni
  • Barcelona na hangen Enrique Ko Arteta Wasanni
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.