Jam’iyyar APC ta cire tsohon gwamnan jihar Benue, Gabriel Suswam, da wasu ‘yan takarar kujerar Sanata biyar daga cikin jerin sunayen ƙarshe da ta miƙa wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).
Haka kuma, jam’iyyar ta cire tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Ondo, Gbenga Elegbeleye, tare da maye gurbin wasu ‘yan takarar majalisar wakilai guda 19 da suka yi nasara a zaɓen fidda gwani da aka gudanar a watan Mayun 2026.
A cikin wata wasiƙa da shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Ajibola Basiru, suka sanya wa hannu, jam’iyyar ta bayyana cewa sauye-sauyen sun biyo bayan rahoton Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafe kan zaɓen fidda gwani.
Jihohin da sauye-sauyen suka shafa sun haɗa da Abia, Kogi, Taraba, Benue, Ebonyi, Ondo, Kaduna, Neja da Kwara.
Sai dai APC ta tabbatar da sunayen wasu fitattun ‘yan takara da za su fafata kujerun Sanata, ciki har da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Jibrin Barau, da gwamnoni AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, Hope Uzodimma na Imo, Ahmadu Fintiri na Adamawa da Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe.
Jam’iyyar ta ce ta karɓi sama da ƙorafe-ƙorafe 700 daga mambobinta dangane da zaɓen fidda gwani. Ta ƙara da cewa a halin yanzu fifikonta shi ne tabbatar da cewa duk ‘yan takarar sun cike takardun tsayawa takara tare da loda su a manhajar INEC kafin cikar wa’adin ranar 10 ga Yulin 2026.


