Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

APC Ta Sauya Jerin ‘Yan Takararta Bayan Nazarin Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Fidda Gwani
Published: July 1, 2026 at 9:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC ta cire tsohon gwamnan jihar Benue, Gabriel Suswam, da wasu ‘yan takarar kujerar Sanata biyar daga cikin jerin sunayen ƙarshe da ta miƙa wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Haka kuma, jam’iyyar ta cire tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Ondo, Gbenga Elegbeleye, tare da maye gurbin wasu ‘yan takarar majalisar wakilai guda 19 da suka yi nasara a zaɓen fidda gwani da aka gudanar a watan Mayun 2026.

A cikin wata wasiƙa da shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Ajibola Basiru, suka sanya wa hannu, jam’iyyar ta bayyana cewa sauye-sauyen sun biyo bayan rahoton Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafe kan zaɓen fidda gwani.

Jihohin da sauye-sauyen suka shafa sun haɗa da Abia, Kogi, Taraba, Benue, Ebonyi, Ondo, Kaduna, Neja da Kwara.

Sai dai APC ta tabbatar da sunayen wasu fitattun ‘yan takara da za su fafata kujerun Sanata, ciki har da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Jibrin Barau, da gwamnoni AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, Hope Uzodimma na Imo, Ahmadu Fintiri na Adamawa da Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe.

Jam’iyyar ta ce ta karɓi sama da ƙorafe-ƙorafe 700 daga mambobinta dangane da zaɓen fidda gwani. Ta ƙara da cewa a halin yanzu fifikonta shi ne tabbatar da cewa duk ‘yan takarar sun cike takardun tsayawa takara tare da loda su a manhajar INEC kafin cikar wa’adin ranar 10 ga Yulin 2026.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas
Next Post: NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.