Pantami Ya Yi Watsi da Amincewa da Jamilu Gwamna a Matsayin Dan Takarar Gwamnan APC a Gombe
Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi watsi da amincewa da Jamilu Ishiyaku Gwamna a matsayin dan takarar gwamnan Jam’iyyar APC a Jihar Gombe domin zaben shekarar 2027.
Wannan na zuwa ne bayan da Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya jagoranci masu ruwa da tsaki na jam’iyyar wajen amincewa da Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin dan takarar hadin kai.
A cikin wata sanarwa da Farfesa Suleiman Mohammed ya sanya wa hannu a madadin kungiyar Pantamiyya, Pantami ya bayyana cewa wannan mataki ya saba wa tanade-tanaden Electoral Act 2026.
Ya jaddada cewa dole ne a bi doka da ka’idojin jam’iyya wajen zaben ‘yan takara, yana mai gargadin cewa duk wani mataki da ya sabawa dokar zabe na iya haifar da rikici a cikin jam’iyya tare da jawo kalubalen shari’a.
Wannan lamari na nuni da yiwuwar sabani a cikin Jam’iyyar APC a jihar Gombe gabanin zaben gwamna na shekarar 2027.


