Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna
Published: May 3, 2026 at 7:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Pantami Ya Yi Watsi da Amincewa da Jamilu Gwamna a Matsayin Dan Takarar Gwamnan APC a Gombe

Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi watsi da amincewa da Jamilu Ishiyaku Gwamna a matsayin dan takarar gwamnan Jam’iyyar APC a Jihar Gombe domin zaben shekarar 2027.

Wannan na zuwa ne bayan da Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya jagoranci masu ruwa da tsaki na jam’iyyar wajen amincewa da Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin dan takarar hadin kai.

A cikin wata sanarwa da Farfesa Suleiman Mohammed ya sanya wa hannu a madadin kungiyar Pantamiyya, Pantami ya bayyana cewa wannan mataki ya saba wa tanade-tanaden Electoral Act 2026.

Ya jaddada cewa dole ne a bi doka da ka’idojin jam’iyya wajen zaben ‘yan takara, yana mai gargadin cewa duk wani mataki da ya sabawa dokar zabe na iya haifar da rikici a cikin jam’iyya tare da jawo kalubalen shari’a.

Wannan lamari na nuni da yiwuwar sabani a cikin Jam’iyyar APC a jihar Gombe gabanin zaben gwamna na shekarar 2027.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna
Next Post: Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
An Watse A Tattaunawar Tsakanin Rasha Da Ukraine Batare Da Cimma Matsaya Ba Labarai
Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.