Jam’iyyar APC a Jihar Gombe ta sanar da Jamilu Ishiyaku Gwamna a matsayin dan takarar gwamna na bai daya domin zaben shekarar 2027.
Sanarwar ta fito ne a ranar Lahadi bayan tuntuba da shawarwari tsakanin gwamnan jihar da sauran manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.
A cewar majiyoyi daga cikin jam’iyyar, an cimma matsaya ne bayan nazari da duba cancanta da karfin ‘yan takarar da suka nuna sha’awar tsayawa takara.
Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Pantami, wanda shima ya nuna sha’awar tsayawa takarar, bai samu goyon bayan zama dan takarar bai daya ba, yayin da aka zabi Jamilu Gwamna a matsayin wanda zai wakilci jam’iyyar.
Masu ruwa da tsaki sun bayyana cewa zaben Gwamna a matsayin dan takarar bai daya zai taimaka wajen hada kan jam’iyyar da kuma kara mata karfi gabanin babban zaben 2027.
Ana sa ran jam’iyyar APC za ta fara shirye-shiryen yakin neman zabe da wuri domin tabbatar da nasara a zaben da ke ta


