Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
Published: April 17, 2026 at 12:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda jimillar kuɗaɗen da za a kashe a cikinsa suka kai naira triliyan 68.32.

Haka kuma, Shugaban ya sanya hannu kan dokar tsawaita lokacin aiwatar da ayyukan babban birnin na kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris, 2026, zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.

Yadda Aka Rarraba Kasafin Kuɗin 2026

A cikin wannan gagarumin kasafi na naira triliyan 68.32, an ware Naira triliyan 4.799 Domin ayyukan da doka ta tanada (Statutory Transfers), sai Naira triliyan 15.8 Domin biyan basussukan da ake bin ƙasa. Naira triliyan 15.4 Domin kuɗaɗen gudanarwa (Recurrent Expenditure), sai Naira triliyan 32.2 Domin ayyukan raya ƙasa (Capital Expenditure).

Wannan kasafi ya nuna cewa kusan kashi 50 cikin ɗari na kuɗaɗen za su tafi ne ga ayyukan raya ƙasa, wanda hakan ke nuna ƙudurin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa tattalin arziki, tsaro, da gina ababen more rayuwa ga ‘yan Najeriya.

Tsawaita Lokacin Kasafin 2025

Baya ga sabon kasafin, Shugaba Tinubu ya amince da gyaran dokar kasafin 2025 domin ba da damar ci gaba da amfani da kuɗaɗen ayyukan raya ƙasa har zuwa ƙarshen watan Yunin 2026.

Manufar wannan mataki ita ce tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs) sun kammala manyan ayyukan da suke hannunsu ba tare da cikas ba, musamman waɗanda suka riga suka yi nisa.

Umarni Zuwa Ga Ma’aikatu

Shugaba Tinubu ya bayar da umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen cikin gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da cewa kowace kwabo ta yi amfanin da aka nufa don amfanin talaka.

Haka kuma, ya jinjina wa shugabanni da mambobin Majalisar Dokoki ta Ƙasa bisa jajircewa da kishin ƙasa da suka nuna wajen hanzarta duba tare da amincewa da wannan kasafi.

A ƙarshe, Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da yin gyare-gyare a ɓangaren tattalin arziki don samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
Next Post: Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Karin Labarai Masu Alaka

Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi Labarai
Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8 Afrika
  • Amurka Tasakawa Sojin Rwanda Takunkumi Afrika
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23 Afrika
  • Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
  • Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
  • Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.