Ranar Asabar kasar Isra’ila ta ce ta kai hare- hare birnin Tehran, inda tayi hankoren abinda tace gininnukan more rayuwa ne, mallakin gwamnatin Iran.
Isra’ila ta kuma Kai hari kasar Lebanon, inda taci gaba da yaki da kungiyar Hezbollah, da Iran ke marawa baya. ‘Yan jarida uku ‘yan kasar Lebanon sun rasa rayukan su a harin, a cewar gidan talabijin na Manar a Lebanon.
Iran itama ta ci gaba da kai hare-hare, inda ta kai farmaki wani sansanin sojin sama a Saudiyya ta jikkata sojojin Amurka 12.


