Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Published: December 18, 2025 at 10:22 AM | By: Bala Hassan

Najeriya ta yi zargin cewa Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa marasa cancanta a gasar cin kofin duniya

Najeriya ta mika takardar koke ga FIFA tana zargin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa da basu cancantaba a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta Afirka a shekara mai zuwa, in ji mai magana da yawun hukumar (NFF).

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta doke Najeriya a bugun fenariti a watan da ya gabata don ci gaba da rayuwa a fatanta na fitowa gasar a Arewacin Amurka, kuma za ta fafata a gasar share fagen shiga gasar tsakanin kungiyoyin kwallon kafa a watan Maris inda kungiyoyi shida za su bi sahun matsayi biyu a gasar karshe ta kungiyoyi 48.

NFF ta ce ‘yan wasa da dama ‘yan kasa suna da takardadun izinin kasashe biyu sun bugawa DR Congo wasa ba tare da cika sharuddan da ake bukata ba.

“Dokokin Congo sun ce ba za ka iya samun ‘yan kasa biyu ba,” in ji babban sakataren NFF Mohammed Sanusi ga manema labarai.

“Akwai da yawa daga cikinsu da ke da fasfo na Turai, wasu daga cikinsu fasfo na Faransa, wasu kuma fasfo na Holland.

“Dokokin FIFA sun ce da zarar ka mallaki fasfo na kasarka, ka cancanta.

A ganinmu, sun cancanci hakan ne ya sa FIFA ta wanke su.

“Amma hujjarmu ita ce an yaudari FIFA har ta wanke su domin ba alhakin FIFA ba ne ta tabbatar da cewa an bi ƙa’idodin Congo.”

“FIFA tana bin ƙa’idodinta ne, bisa ga abin da aka gabatar wa FIFA ne ya suka wanke su, mu a wajanmu muna cewa an yi zamba ne.”

 

 

 

 

 

 

 

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo ta yi watsi da zarge-zargen da ake ma ta.

“Idan ba za ku iya cin nasara a filin wasa ba, to kada ku yi ƙoƙarin cin nasara daga ƙofar baya,” in ji Hukumar ƙwallon ƙafa ta Kongo (Fecofa) a wani rubutu da ta yi a shafukan sada zumunta.

“Dole ne a buga gasar cin kofin duniya da mutunci da kwarin gwiwa. Ba tare da dabaru na shari’a ba da ku kawo shi.”

FIFA ba ta amsa buƙatar yin tsokaci nan take ba saboda lokutan aiki.

Gasar cin kofin duniya za ta gudana a Amurka, Kanada da Mexico daga 11 ga Yuni zuwa 19 ga Yuli.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Next Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Baital Malin Amurka Tace Sahannun Trump Zai Fito A Kudin Kasar Amurka
  • Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
  • Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
  • Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.