Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Published: December 18, 2025 at 10:22 AM | By: Bala Hassan

Najeriya ta yi zargin cewa Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa marasa cancanta a gasar cin kofin duniya

Najeriya ta mika takardar koke ga FIFA tana zargin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa da basu cancantaba a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta Afirka a shekara mai zuwa, in ji mai magana da yawun hukumar (NFF).

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta doke Najeriya a bugun fenariti a watan da ya gabata don ci gaba da rayuwa a fatanta na fitowa gasar a Arewacin Amurka, kuma za ta fafata a gasar share fagen shiga gasar tsakanin kungiyoyin kwallon kafa a watan Maris inda kungiyoyi shida za su bi sahun matsayi biyu a gasar karshe ta kungiyoyi 48.

NFF ta ce ‘yan wasa da dama ‘yan kasa suna da takardadun izinin kasashe biyu sun bugawa DR Congo wasa ba tare da cika sharuddan da ake bukata ba.

“Dokokin Congo sun ce ba za ka iya samun ‘yan kasa biyu ba,” in ji babban sakataren NFF Mohammed Sanusi ga manema labarai.

“Akwai da yawa daga cikinsu da ke da fasfo na Turai, wasu daga cikinsu fasfo na Faransa, wasu kuma fasfo na Holland.

“Dokokin FIFA sun ce da zarar ka mallaki fasfo na kasarka, ka cancanta.

A ganinmu, sun cancanci hakan ne ya sa FIFA ta wanke su.

“Amma hujjarmu ita ce an yaudari FIFA har ta wanke su domin ba alhakin FIFA ba ne ta tabbatar da cewa an bi ƙa’idodin Congo.”

“FIFA tana bin ƙa’idodinta ne, bisa ga abin da aka gabatar wa FIFA ne ya suka wanke su, mu a wajanmu muna cewa an yi zamba ne.”

 

 

 

 

 

 

 

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo ta yi watsi da zarge-zargen da ake ma ta.

“Idan ba za ku iya cin nasara a filin wasa ba, to kada ku yi ƙoƙarin cin nasara daga ƙofar baya,” in ji Hukumar ƙwallon ƙafa ta Kongo (Fecofa) a wani rubutu da ta yi a shafukan sada zumunta.

“Dole ne a buga gasar cin kofin duniya da mutunci da kwarin gwiwa. Ba tare da dabaru na shari’a ba da ku kawo shi.”

FIFA ba ta amsa buƙatar yin tsokaci nan take ba saboda lokutan aiki.

Gasar cin kofin duniya za ta gudana a Amurka, Kanada da Mexico daga 11 ga Yuni zuwa 19 ga Yuli.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Next Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
  • Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.