Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Published: December 18, 2025 at 10:22 AM | By: Bala Hassan

Najeriya ta yi zargin cewa Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa marasa cancanta a gasar cin kofin duniya

Najeriya ta mika takardar koke ga FIFA tana zargin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa da basu cancantaba a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta Afirka a shekara mai zuwa, in ji mai magana da yawun hukumar (NFF).

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta doke Najeriya a bugun fenariti a watan da ya gabata don ci gaba da rayuwa a fatanta na fitowa gasar a Arewacin Amurka, kuma za ta fafata a gasar share fagen shiga gasar tsakanin kungiyoyin kwallon kafa a watan Maris inda kungiyoyi shida za su bi sahun matsayi biyu a gasar karshe ta kungiyoyi 48.

NFF ta ce ‘yan wasa da dama ‘yan kasa suna da takardadun izinin kasashe biyu sun bugawa DR Congo wasa ba tare da cika sharuddan da ake bukata ba.

“Dokokin Congo sun ce ba za ka iya samun ‘yan kasa biyu ba,” in ji babban sakataren NFF Mohammed Sanusi ga manema labarai.

“Akwai da yawa daga cikinsu da ke da fasfo na Turai, wasu daga cikinsu fasfo na Faransa, wasu kuma fasfo na Holland.

“Dokokin FIFA sun ce da zarar ka mallaki fasfo na kasarka, ka cancanta.

A ganinmu, sun cancanci hakan ne ya sa FIFA ta wanke su.

“Amma hujjarmu ita ce an yaudari FIFA har ta wanke su domin ba alhakin FIFA ba ne ta tabbatar da cewa an bi ƙa’idodin Congo.”

“FIFA tana bin ƙa’idodinta ne, bisa ga abin da aka gabatar wa FIFA ne ya suka wanke su, mu a wajanmu muna cewa an yi zamba ne.”

 

 

 

 

 

 

 

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo ta yi watsi da zarge-zargen da ake ma ta.

“Idan ba za ku iya cin nasara a filin wasa ba, to kada ku yi ƙoƙarin cin nasara daga ƙofar baya,” in ji Hukumar ƙwallon ƙafa ta Kongo (Fecofa) a wani rubutu da ta yi a shafukan sada zumunta.

“Dole ne a buga gasar cin kofin duniya da mutunci da kwarin gwiwa. Ba tare da dabaru na shari’a ba da ku kawo shi.”

FIFA ba ta amsa buƙatar yin tsokaci nan take ba saboda lokutan aiki.

Gasar cin kofin duniya za ta gudana a Amurka, Kanada da Mexico daga 11 ga Yuni zuwa 19 ga Yuli.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Next Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu Najeriya
  • Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
  • Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.