Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya
Published: December 15, 2025 at 10:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Aliko Dangote, shugaban masana’antun kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya zargi Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta (NMDPRA), Farouk Ahmed, da cin hanci, yana mai cewa ya biya dala miliyan 5 a matsayin kuɗin makarantar sakandare ga ’ya’yansa huɗu a ƙasar Switzerland.

Dangote ya yi zargin ne a yayin wani taron manema labarai a Matatar Dangote a ranar Lahadi, inda yace irin wannan kashe kuɗi ya wuce ƙarfin albashin shugaban hukumar, tare da kira ga gwamnatin tarayya da ta binciki lamarin.

Attajirin ya ce ya dace a ba Ahmed damar wanke kansa ta hanyar bincike, ba tare da korar sa ba, amma ya yi barazanar ɗaukar matakin shari’a kan makarantun Switzerland idan suka musanta zargin.

A wani bangaren kuma, Dangote ya bayyana cewa farashin man fetur zai ragu zuwa kusan naira 740 kowace lita a Lagos daga ranar Talata, bayan da matatar tasa ta rage farashin zuwa naira 699.

Ya ce tashoshin MRS ne za su fara nuna sabon farashin, yana mai jaddada cewa tace man fetur a cikin gida zai amfani ’yan Najeriya duk da asarar da masu shigo da mai za su tafka a Kasar.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya
Next Post: Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina

Karin Labarai Masu Alaka

Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.