Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50
Published: February 27, 2026 at 10:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Fiye da mutane 50 ‘yan asalin kasar Ghana ne suka rasa rayukan su a yakin da ake fafatawa tsakanin Rasha da Ukrain, bayan da aka yaudare su suka shiga yaki, a cewar ministan harkokin kasashen waje na Ghana Samuel Okudzeto Ablakwa, bayan da ya kai ziyara Kyiv, babban birnin Ukrain, inda ake tattauna maganar daukan ‘yan Afirka yaki.

Rahotanni dake nuna jawo hankalin maza daga Afirka zuwa Rasha kan alkawarin samun aiki, amma sai su bige da yin yaki a sahun gaba sun yi yawa a watannin baya bayan nan, abinda yake jawo gurbacewar alaka tsakanin Rasha da kasashen dake da hannu a ciki.

Hukumomin Rasha sun musanta zargin daukan ‘yan Afirka ba bisa ka’ida ba don yi musu yaki.

A wani taro na manema labarai ranar Talata, da yake tsaye kusa da Alakwa, ministan harkokin wajen Ukrain Andri Sybiha, ya ce fiye da ‘yan Afirka 1780 daga kasashe 36 suke yiwa Rasha yaki.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
Next Post: An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a Sauran Duniya
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
  • Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
  • Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere Labarai
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
  • Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.