Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki
Published: April 5, 2026 at 9:27 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutane biyar sun halaka a Ukraine wasu 19 kuma suka ji rauni sakamakon wani harin da Rasha ta kai da jirgin da bashi da matuki akan wata kasuwa a wani gari dake daf da fagen yakin kasar da Rasha da ake kira Nikopol a ranar Asabar, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin babban lauyan gwamnatin kasar tayi bayani.

Garin Nikopol, mai tazarar ‘yan kilomitoci daga yankin kasar da Rasha ta mamaye dake kan gabar kogin da ake kira Dnipro, ya dade yana fuskantar hare hare daga Rasha.

“Wannan harin wani kari ne kan laifuffukan yaki da Rasha ta ke aikatawa,” inji sanarwar da ofishin babban lauyan gwamnatin kasar ya fitar.

Ahalinda ake ciki kuma, wani hadimin shugaba Volodimyr Zelensky na Ukraine, yace akwai yiwuwar jakadun Amurka na musamman Steve Whitkoff, da Jared Kushner, za su ziyarci Kyiv cikin watan nan, a wani yunkuri na sake farfado da shawarwarin sulhu da Rasha, wanda ya tsaya, sakamakon barkewar yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran
Next Post: Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
  • Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
  • Shirin Ga Fili GA Doki Shirye-Shirye
  • Yeriman Ingila Ya Mayarwa Trump Martani Amurka
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.