Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka
Published: December 15, 2025 at 6:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ko CDEAO, ta bayyana rashi yardarta da shirin mayar da mulki hannun farar hula da shugabannin mulkin soja na Guinea-Bissau, suka bayyana, tana mai bukatar da a gaggauta maido da aiki da tsarin mulki.

Shugabannin ECOWAS, sun yi barazanar saka takunkumi na musamman a kan duk wadanda ke kawo cikas ga maido da mulkin farar hula a kasar.

A ranar 26 ga watan Nuwamba ne wasu hafsoshin soja a Guinea-Bissau suka hambarar da shugaba Umaro Sissoco Embalo, kwana daya kafin a bayyana sakamakon zaben shugaban kasa, kashegari kuma suka ayyana Manjo Janar Horta Inta-a a matsayin shugaban gwamnatin mulkin soja na wuin gadi.

Wannan juyin mulki da aka yi a Gyuinea-Bissau, shine na tara cikin shekaru 5 da suka shige a yankin yammaci da tsakiyar Afirka, abinda ya kara irin fargabar da ake yi ta zaizayewar mulkin dimokuradiyya a wannan yanki mai fama da rashin tsaro da rashin kwanciyar hankalin siyasa.

Shugabannin dake halartar taron kolin shekara na kungiyar ECOWAS ranar lahadi a Abuja, babban birnin Najeriya, sun yi kiran da a sako dukkan ‘yan siyasar da aka kama, ciki har da shugabannin hamayya, a kuma tsara shirin maida mulki cikin gaggawa wanda zai kumshi dukkan sassan kasar cikin gaggawa.

Shugaban majalisar zartasa ta kungiyar ECOWAS, Omar Touray, yace matakin da shugabannin kungiyar suka dauka shine na tabbatar da cewa sam ba za a taba yarda da sauya gwamnati ta hanyar da tsarin mulki bai amince ba.

ECOWAS ta ce ‘yan kallonta, da na Kungiyar Tarayyar Afirka da na kasashe masu magana da harshen Portugal duk sun ce zaben shugaban kasa da aka gudanar a Guinea-Bissau, an yi shi cikin adalci.

Har ila yau kungiyar ta umurci shugabanta da ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’ai zuwa Gyuinea-Bissau domin tattaunawa da hukumomin sojan kasar.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi
Next Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.