Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Published: December 11, 2025 at 6:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitocin Kasafin Kuɗi na Majalisar Dokokin Amurka sun jaddada kudirin Amurka na tunkarar take-taken addini a duniya, musamman a Najeriya.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar tawagar ‘yan majalisar da Shugaba Donald Trump ya tura ƙarƙashin jagorancin Riley Moore.

A Najeriya, tawagar ta gana da mai bawa Shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin ƙarfafa haɗin gwiwar yaki da ta’addanci da tsaro a yankin.

Moore ya kai ziyara Benue, inda ya gana da shugabannin Katolika da na al’ummar Tiv tare da duba sansanonin ‘yan gudun hijira.

Ya bayyana abin da ya gani a matsayin abin tausayi, inda ya ruwaito tashin hankali da kisan gilla da suka tilasta dubban Kiristoci tserewa daga gidajen su.

Ya ce fiye da Kiristoci 600,000 na rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijira a Benue. Moore ya kuma yi zargin “harin kisan kare dangi da Fulani suke yi a jihar.

Tawagar ta yaba wa gwamnatin Najeriya kan ceto daliban makarantar Katolika fiye da 100, tare da cewa ƙawancen tsaro tsakanin Najeriya da Amurka ya fara inganta, amma akwai sauran aikin da za a yi.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da dangantaka ke ƙara tsami bayan gwamnatin Trump ta sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna keta ‘yancin addini, matakin da ya haddasa ce-ce ku-ce a bangaren diplomasiya.

Gwamnatin Tarayya ta ce ba a nuna bambanci ga addini, saboda rashin tsaro yana shafar kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar
Next Post: Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
  • Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Asusun IMF Zasu Ziyarci Kasar Gabon Afrika
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki Afrika
  • Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
  • Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.