Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Published: December 11, 2025 at 6:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitocin Kasafin Kuɗi na Majalisar Dokokin Amurka sun jaddada kudirin Amurka na tunkarar take-taken addini a duniya, musamman a Najeriya.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar tawagar ‘yan majalisar da Shugaba Donald Trump ya tura ƙarƙashin jagorancin Riley Moore.

A Najeriya, tawagar ta gana da mai bawa Shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin ƙarfafa haɗin gwiwar yaki da ta’addanci da tsaro a yankin.

Moore ya kai ziyara Benue, inda ya gana da shugabannin Katolika da na al’ummar Tiv tare da duba sansanonin ‘yan gudun hijira.

Ya bayyana abin da ya gani a matsayin abin tausayi, inda ya ruwaito tashin hankali da kisan gilla da suka tilasta dubban Kiristoci tserewa daga gidajen su.

Ya ce fiye da Kiristoci 600,000 na rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijira a Benue. Moore ya kuma yi zargin “harin kisan kare dangi da Fulani suke yi a jihar.

Tawagar ta yaba wa gwamnatin Najeriya kan ceto daliban makarantar Katolika fiye da 100, tare da cewa ƙawancen tsaro tsakanin Najeriya da Amurka ya fara inganta, amma akwai sauran aikin da za a yi.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da dangantaka ke ƙara tsami bayan gwamnatin Trump ta sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna keta ‘yancin addini, matakin da ya haddasa ce-ce ku-ce a bangaren diplomasiya.

Gwamnatin Tarayya ta ce ba a nuna bambanci ga addini, saboda rashin tsaro yana shafar kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar
Next Post: Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
  • China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.