Gwamnatin jihar Jigawa ta bayyana cewa ta samu raguwar matakin talauci da kashi 15 cikin 100 a fadin jihar, sakamakon matakan bunkasa tattalin arziki da ta dauka a baya-bayan nan.
Gwamnatin ta ce wannan nasara na nuna yadda shirye shiryenta ke fara haifar da da mai ido.
Gidan Rediyon jihar Jigawa ya rawaito cewa Gwamnan jihar, Dakta Umar Namadi, ne ya bayyana hakan a Birnin Kudu yayin bude babban kantin sayar da kayayyaki mai suna Akilu Aliyu Multipurpose Shopping Complex. Gwamnan ya ce wani rahoton bincike da aka kammala a watan Satumba na shekarar da ta gabata ne ya nuna raguwar talauci a jihar.
Gwamna Umar Namadi ya kara da cewa gwamnatin jihar ta tallafa wa kimanin mutane dubu 400 ta hanyar shirye-shiryen samar da ayyukan yi, yayin da kananan da matsakaitan ’yan kasuwa kusan dubu 230 suka amfana da rancen kudi daga Bankin Raya Masana’antu domin bunkasa harkokinsu.
Ya jaddada cewa gwamnatin Jigawa za ta ci gaba da bai wa kungiyoyi da daidaikun mutane goyon baya domin kara samar da ayyukan yi da bunkasa tattalin arzikin jihar.


