Wani Harin da aka kai a makarantar ‘yan mata ta Iran wanda ya yi sanadin mutuwar yara da dama na iya kasancewa sakamakon amfani da bayanan da Amurka ta yi amfani da su a baya, kamar yadda wasu majiyoyi biyu da ke da masaniya kan lamarin suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters a ranar Laraba, inda suka ba da sabbin bayanai game da abin da zai kasance cikin mafi muni da fararen hula suka rasa rayukansu cikin shekaru da dama da aka shafe ana gwabzawa da Amurka.
Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton farko a yau alhamis cewa wani bincike na cikin gida na sojojin Amurka da ke ci gaba da gudana ya nuna cewa akwai yiwuwar sojojin Amurka ne suka kai harin da aka kai makarantar ‘yan matan da ke Minab.
Kamar yadda wani Bidiyo da ya fito wanda masana suka ce da alama ya nuna makami mai linzami na Amurka Tomahawk ya afkawa yankin. Sai dai ba a san ainihin yadda lamarin ya faru ba, kuma ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta ki cewa komai, tana mai cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.
Harin wanda aka kai a rana ta farko ta harin da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, ya kashe dalibai 150, a cewar jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, Ali Bahreini.


