Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona!
Published: January 4, 2026 at 1:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Jagoran Tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bukaci Gwamna Abba K. Yusuf da ya bar kujerar gwamna idan har yana shirin ficewa daga jam’iyyar NNPP.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wani taro da magoya bayansa da masu ruwa da tsaki a Kano, a daidai lokacin da ake rade-radin cewa gwamnan na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Ya ce ba daidai ba ne a kwace wa tafiyar Kwankwasiyya kujerar gwamna daya tilo da take da shi a fadin Najeriya.

“Idan APC tana da kusan gwamnoni 30, me ya sa sai gwamnan Kano? Shi ne kadai ya rage mana,” in ji Kwankwaso, yana mai cewa duk wanda ke tursasa gwamnan ya sauya sheka ya kamata ya gaya masa ya bar kujerar gwamna ya tafi.

Tsohon gwamnan ya bayyana halin da ake ciki a siyasar Kano a matsayin abin tayar da hankali, yana mai gargadin cewa rikicin ba zai amfani jihar ba.

Ya ce yana kokarin sasanta al’amura a bayan fage domin hana jihar fadawa matsala.

Kwankwaso ya jaddada cewa gwamnatin NNPP har yanzu tana da lokaci ta yi wa al’umma aiki, yana mai kira da a hada kai maimakon rikici, sannan kuma yayi Suka game da kiran komawa abin da ya kira “Gandujiyya”, yana mai cewa hakan ya nuna rarrabuwar siyasa a jihar.

Ya karyata ikirarin cewa NNPP ba ta da karfi a Kano, yana mai cewa jam’iyyar ce mafi rinjaye.

Jagoran Jam’iyar ya gargadi shugabancin APC da kada su raina Kano, yana mai cewa jihar na da muhimmanci kuma ya kamata a rika mu’amala da ita cikin taka-tsantsan.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC
Next Post: Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe

Karin Labarai Masu Alaka

Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.