Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona!
Published: January 4, 2026 at 1:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Jagoran Tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bukaci Gwamna Abba K. Yusuf da ya bar kujerar gwamna idan har yana shirin ficewa daga jam’iyyar NNPP.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wani taro da magoya bayansa da masu ruwa da tsaki a Kano, a daidai lokacin da ake rade-radin cewa gwamnan na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Ya ce ba daidai ba ne a kwace wa tafiyar Kwankwasiyya kujerar gwamna daya tilo da take da shi a fadin Najeriya.

“Idan APC tana da kusan gwamnoni 30, me ya sa sai gwamnan Kano? Shi ne kadai ya rage mana,” in ji Kwankwaso, yana mai cewa duk wanda ke tursasa gwamnan ya sauya sheka ya kamata ya gaya masa ya bar kujerar gwamna ya tafi.

Tsohon gwamnan ya bayyana halin da ake ciki a siyasar Kano a matsayin abin tayar da hankali, yana mai gargadin cewa rikicin ba zai amfani jihar ba.

Ya ce yana kokarin sasanta al’amura a bayan fage domin hana jihar fadawa matsala.

Kwankwaso ya jaddada cewa gwamnatin NNPP har yanzu tana da lokaci ta yi wa al’umma aiki, yana mai kira da a hada kai maimakon rikici, sannan kuma yayi Suka game da kiran komawa abin da ya kira “Gandujiyya”, yana mai cewa hakan ya nuna rarrabuwar siyasa a jihar.

Ya karyata ikirarin cewa NNPP ba ta da karfi a Kano, yana mai cewa jam’iyyar ce mafi rinjaye.

Jagoran Jam’iyar ya gargadi shugabancin APC da kada su raina Kano, yana mai cewa jihar na da muhimmanci kuma ya kamata a rika mu’amala da ita cikin taka-tsantsan.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC
Next Post: Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe

Karin Labarai Masu Alaka

Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
  • Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.