Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC
Published: January 3, 2026 at 9:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Dalilan da su ka sanya sauya shekar Gwamna Abba zuwa APC ya samu tsaiko.

An gano dalilan da suka sa aka dage sauyin sheƙar Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, bayan an riga an kammala shirye-shirye na farko.

A ranar Juma’a, wasu majiyoyi sun rawaito cewa gwamnan ya kammala shirye-shiryen sanar da sauyin jam’iyyarsa zuwa APC a ranar Litinin.

Kafin a dage batun sauyin jam’iyyar, hedikwatar jam’iyyar APC ta ƙasa ta shirya cewa gwamnan zai zama mutum na farko da za a yi wa rajista a Kano a sabon tsarin rajistar yanar gizo na jam’iyyar.

Bisa tsarin da aka fara tsara wa, tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, ne zai raka gwamnan zuwa mazabarsa ta Diso domin yin rajista a shafin yanar gizon jam’iyyar tare da karɓar katin jam’iyya.

Bayan kammala rajistar gwamnan, an shirya cewa nan take zai raka Ganduje zuwa garinsa na asali a karamar hukumar Dawakin Tofa domin sabunta rajistarsa a sabon shafin yanar gizon jam’iyyar.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa Shugaba Bola Tinubu ne ya bayar da umarnin a dakatar da sauyin shekar ta Abba har sai an yi ƙoƙari wajen shawo kan uban gidansa na siyasa, Rabiu Kwankwaso.

A cewar majiyoyin, shirin Kwankwaso na sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC ya sauya lissafin APC.

“Fadar Shugaban Ƙasa na da bayanan sirri cewa Kwankwaso ya gana da Obasanjo da Peter Obi, kuma akwai yiyuwar su haɗa kai domin kalubalantar Tinubu a 2027 kuma  Tikitin Obi/Kwankwaso haɗin gwiwa ne mai ƙarfi da zai iya sauya ma’aunin siyasar APC.

“Kuma idan babu Kwankwaso, ƙarfin siyasar gwamnan zai ragu, saboda haka Tinubu na sake tunani kan sauyin jam’iyyar Gwamna Yusuf.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida wa wannan jarida cewa gwamnan da kansa ne ya nemi ƙarin lokaci domin ya samu damar shawo kan ƙarin mambobin Majalisar Dokoki ta Jiha da ta Ƙasa su bi sahunsa wajen sauyin jam’iyyar.

Wasu majiyoyi da ba a tabbatar da su ba sun kuma shaida cewa matsin lambar da gwamnan ke fuskanta ta sanya shi cikin ruɗani, har ta kai ga yana tunanin janye batun sauyin jam’iyyar tare da komawa ya sake haɗewa da uban gidansa Kwankwaso.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico!
Next Post: Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona!

Karin Labarai Masu Alaka

Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani Afrika
An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi Afrika
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.