Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Published: December 26, 2025 at 1:33 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

A bisa rokon hukumomin Najeriya, mayakan Amurka sun kai hare-hare ta sama a kan sansanonin da aka ce na ‘yan kungiyar Daesh, ko ISIS ne, a jihar Sakkwato dake yankin arewa maso yammacin kasar cikin daren nan da ya shige.

Rahoton farko game da wannan harin ya fito ne daga bakin shugaba Donald Trump na Amurka wanda ya ce a bisa umurninsa, Amurka ta kai munanan hare-hare ta sama a kan ‘yan ISIS wadanda a cewarsa su na kashe kiristoci a yankin.

Daga bisani, rundunar sojojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta fito da wata sanarwar dake cewa an kai wannan harin ne bisa rokon hukumomin Najeriya, kuma an kashe ‘yan ISIS da dama.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, ta fitar da sanarwa dazun nan tana fadin cewa wannan harin da aka kai ya samo asali ne daga yarjejeniyar hadin kan tsaro da musanyar bayanan leke asiri.

Wata sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya bayar cikin daren nan, ta tabbatar da cewa lallai Najeriya ce ta bukaci a kai wannan hari kan sansanonin ‘yan ta’addar a karkashin yarjejeniyar hadin kan tsaron da ta kulla da Amurka da nufin shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi yankin arewa maso yammacin Najeriya.

Ma’aikatar ta ce gwamnatin Najeriya zata ci gaba da yin aiki da kawayenta ta hanyoyin diflomasiyya da tsaro domin nakkasa ‘yan ta’adda da ayyukansu na ta’addanci a kasar.

A ranar litinin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da labarin ewa tun a cikin watan Nuwamba Amurka ta fara shawagin leken asiri a sassa masu yawa na Najeriya.

Gwamnatin Najeriya ta ce wadannan ‘yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda ba su ware addini, suna kai hare-harensu a kan Musulmi da kiruista, kuma ikirarin da Amurka keyi na cewa ana kisan kare dangi ma kirista babu ka mshin gaskiya a cikinsa.

Najeriya ta yarda zata yi aiki da Amurka wajen karfafa yakar wadannan ‘yan ta’adda.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa
Next Post: Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe Afrika
Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • Baital Malin Amurka Tace Sahannun Trump Zai Fito A Kudin Kasar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.