Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Published: December 26, 2025 at 1:33 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

A bisa rokon hukumomin Najeriya, mayakan Amurka sun kai hare-hare ta sama a kan sansanonin da aka ce na ‘yan kungiyar Daesh, ko ISIS ne, a jihar Sakkwato dake yankin arewa maso yammacin kasar cikin daren nan da ya shige.

Rahoton farko game da wannan harin ya fito ne daga bakin shugaba Donald Trump na Amurka wanda ya ce a bisa umurninsa, Amurka ta kai munanan hare-hare ta sama a kan ‘yan ISIS wadanda a cewarsa su na kashe kiristoci a yankin.

Daga bisani, rundunar sojojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta fito da wata sanarwar dake cewa an kai wannan harin ne bisa rokon hukumomin Najeriya, kuma an kashe ‘yan ISIS da dama.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, ta fitar da sanarwa dazun nan tana fadin cewa wannan harin da aka kai ya samo asali ne daga yarjejeniyar hadin kan tsaro da musanyar bayanan leke asiri.

Wata sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya bayar cikin daren nan, ta tabbatar da cewa lallai Najeriya ce ta bukaci a kai wannan hari kan sansanonin ‘yan ta’addar a karkashin yarjejeniyar hadin kan tsaron da ta kulla da Amurka da nufin shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi yankin arewa maso yammacin Najeriya.

Ma’aikatar ta ce gwamnatin Najeriya zata ci gaba da yin aiki da kawayenta ta hanyoyin diflomasiyya da tsaro domin nakkasa ‘yan ta’adda da ayyukansu na ta’addanci a kasar.

A ranar litinin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da labarin ewa tun a cikin watan Nuwamba Amurka ta fara shawagin leken asiri a sassa masu yawa na Najeriya.

Gwamnatin Najeriya ta ce wadannan ‘yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda ba su ware addini, suna kai hare-harensu a kan Musulmi da kiruista, kuma ikirarin da Amurka keyi na cewa ana kisan kare dangi ma kirista babu ka mshin gaskiya a cikinsa.

Najeriya ta yarda zata yi aiki da Amurka wajen karfafa yakar wadannan ‘yan ta’adda.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa
Next Post: Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
  • Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
  • Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
  • Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye Afrika
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.