Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi
Published: November 30, 2025 at 7:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Zamu tabbatar da kawo karshen hadura a lokacin Bukukuwan karshen shekara – inji Jami’an Hukumar kiyaye hadura a Gombe.

Hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jihar Gombe ta shirya taron fadakar da jama’a game da illar gudu fiye da kima, tare da tukin ganganci yayin bukukuwan karshen shekara.

Kwamandan hukumar kiyaye hadura a jihar Gombe, Mr Samson Kaura ne ya bayyana haka lokacin jawabi ga direbobi da sauran jama’a, yayin gangamin a dakin taro na tashar Dankwanbo Mega Park dake Gombe.

Mr. Kaura, ya tabbatar da cewa ana samun yawan tafiye tafiye a karshen shekara, a saboda haka yabukaci masu ababen hawa da su rika lura tare da bin ka’idojin hanya domin kare rayuwar al’umma.

Ya tabbatar da cewa, ansamu hadura fiye da arba’in da shida a tsakiyar wannan shekarar, kuma mutane sha bakwai sun mutu a jihar Gombe.

A jawaban su, shugaban riko na tashar Dankwanbo Mega Park Malam Sani Sabo da shugaban kungiyar ‘yan achaba a jihar Gombe, Malam Kabiru Jafaru sun bukaci gwamnati da tayi la’akari da gyara hanyoyi da suka lalace a jihar domin gujewa samun hadura.

Malam Sani Sabo da Kabiru Jafaru, sun lissafo hanyar Gombe zuwa Dukku zuwa Darazo, hanyar Gombe zuwa Biu zuwa Maiduguri da hanyar Gombe zuwa Bauchi a matsayin hanyoyi masu muni. Wanda kuma suna haifar da hadura saboda lalacewar su, Inda su kayi fatan gwamnati zata kawo karshen wannan wahalhalu da jama’a ke fuskanta.

A nasu bangaren, daraktar hukumar wayar da kan al’umma jihar Gombe Miss Adalin Waye Patari, shugaban Direbobi na NURTW Malam Musa Yunusa da hakimin Kagarawal Alhaji Usman Ali sun bukaci Direbobi dasu gujewa shaye-shaye a yayin tuki, tare da yawaita gudu fiye da kima.

Inda suka tabbatar da cigaba da fadakar da mambobin su da jama’ar gari domin gujewa samun hadura a fadin kasar nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Next Post: Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Sakamakon Yakin Gabas Ta Tsakiya Kowacce Gangar Mai Ta Haura Dala 100 Afrika
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
  • Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.