Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Published: November 30, 2025 at 3:34 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Mataimakin Shugaban jami’ar jihar Gombe Ferfesa Sani Yauta ya kaddamar da littafi mai take Sauye-Sauye a bangaren ilimi da shugabanci.

Jami’ar Gombe (GSU) ta gudanar da bikin kaddamar da sabon littafi mai suna “Dynamics of Educational Administration and Planning” wanda Farfesa Sani Ahmed Yauta ya rubuta, a dakin taro na Haruna Kadir Rasheed dake jami’ar.

Taron ya sami halartar jami’an gwamnati, malamai, da baki na musamman.

Shugaban taron, mataimakin Gwamnan Jihar Gombe, Dr. Manassah Daniel Jatau, ya yabawa Farfesa Yauta bisa wannan gudummawar ilimi da ya bayar a sashin ilimi.

Fitattun jami’an gwamnati sun halarci bikin, ciki har da shugaban ma’aikata na jihar Gombe, Alhaji Ahmed Kasimu Abdullahi, Shugaban Jami’ar Tarayya dake Kashere, Farfesa Umaru Pate, Shugaban Jami’ar Lincoln University, Farfesa Adamu Sadiq Abubakar da Shugabar kwalejin koyon jinya, tare da wasu shugabannin cibiyoyi a jihar.

Haka zalika, Daraktan Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Farfesa Yusuf Muhammed Abdullahi, ya hallarci bikin tare da sauran manyan baki.

A jawabin sa, Babban Mai Kaddamarwa, Arc. Yunusa Yakubu, ya jinjina wa Farfesa Yauta kan jajircewarsa wajen bunkasa ilimi, yana mai bayyana littafin a matsayin abin dogaro ga masu gudanarwa, masu bincike da masu tsara manufofin ilimi.

Littafin dai wata dama ce da mahukunta zasu iya amfani da ita don sabutan tsari da manhajoji da ake amfani da su a makarantu a kasar baki daya. An kuma ja hankalin sauran malamai a fannin ilimi da su bada irin wadannan gudumawar don habaka ilimi, da ganin an samar da yanayi wanda ilimi a kasar zai yi gogayya da kasashe masu cigaba a fanin ilimi.

Kabatar da kasidu da taron karawa juna sani irin wadannan na da matukara muhimanci ga cigaban ilimi, ta haka ma ana iya sako daliban ilimi wajen shirya irin wadannan tarukan, da muna musu makamar aiki; a cewar daya daga cikin mahalarta taron.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Next Post: Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan Labarai
  • Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
  • Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
  • Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.