Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Published: November 30, 2025 at 3:34 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Mataimakin Shugaban jami’ar jihar Gombe Ferfesa Sani Yauta ya kaddamar da littafi mai take Sauye-Sauye a bangaren ilimi da shugabanci.

Jami’ar Gombe (GSU) ta gudanar da bikin kaddamar da sabon littafi mai suna “Dynamics of Educational Administration and Planning” wanda Farfesa Sani Ahmed Yauta ya rubuta, a dakin taro na Haruna Kadir Rasheed dake jami’ar.

Taron ya sami halartar jami’an gwamnati, malamai, da baki na musamman.

Shugaban taron, mataimakin Gwamnan Jihar Gombe, Dr. Manassah Daniel Jatau, ya yabawa Farfesa Yauta bisa wannan gudummawar ilimi da ya bayar a sashin ilimi.

Fitattun jami’an gwamnati sun halarci bikin, ciki har da shugaban ma’aikata na jihar Gombe, Alhaji Ahmed Kasimu Abdullahi, Shugaban Jami’ar Tarayya dake Kashere, Farfesa Umaru Pate, Shugaban Jami’ar Lincoln University, Farfesa Adamu Sadiq Abubakar da Shugabar kwalejin koyon jinya, tare da wasu shugabannin cibiyoyi a jihar.

Haka zalika, Daraktan Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Farfesa Yusuf Muhammed Abdullahi, ya hallarci bikin tare da sauran manyan baki.

A jawabin sa, Babban Mai Kaddamarwa, Arc. Yunusa Yakubu, ya jinjina wa Farfesa Yauta kan jajircewarsa wajen bunkasa ilimi, yana mai bayyana littafin a matsayin abin dogaro ga masu gudanarwa, masu bincike da masu tsara manufofin ilimi.

Littafin dai wata dama ce da mahukunta zasu iya amfani da ita don sabutan tsari da manhajoji da ake amfani da su a makarantu a kasar baki daya. An kuma ja hankalin sauran malamai a fannin ilimi da su bada irin wadannan gudumawar don habaka ilimi, da ganin an samar da yanayi wanda ilimi a kasar zai yi gogayya da kasashe masu cigaba a fanin ilimi.

Kabatar da kasidu da taron karawa juna sani irin wadannan na da matukara muhimanci ga cigaban ilimi, ta haka ma ana iya sako daliban ilimi wajen shirya irin wadannan tarukan, da muna musu makamar aiki; a cewar daya daga cikin mahalarta taron.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Next Post: Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
  • ‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.