Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara
Published: July 7, 2026 at 6:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Yobe dake arewa maso Gabashin Najeriya ta sake jaddada aniyarta na rage yawan mutuwar yara masu ƙasa da shekara biyar ta hanyar ci gaba da aiwatar da shirin SARMAAN, tare da shirye-shiryen faɗaɗa shi zuwa dukkan ƙananan hukumomi 17 na jihar.

Ana gudanar da shirin ne na haɗin gwiwa da African Field Epidemiology Network (AFENET) Nigeria, inda aka faɗaɗa shi daga ƙananan hukumomi 10 a matakin farko zuwa 13 a zagayen da ake gudanarwa a halin yanzu.

Babban Jami’in Hulɗa da Gwamna kan Kula da Lafiya a Matakin Farko, Dakta Umar Ciroma, ya ce shirin ya samo asali ne daga shawarar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ga ƙasashen da ke fama da yawan mutuwar yara masu ƙasa da shekara biyar.

Ya bayyana cewa ana bai wa yara ƙwayar maganin Azithromycin sau shida cikin tsawon shekaru uku, ana ba su duk bayan watanni shida, domin kariya daga wasu cututtukan ƙwayoyin bacteria da ke haddasa ciwon huhu, cutar sepsis, cututtukan fata, trachoma da kuma wasu nau’ikan gudawa.

Al’ummomi da dama a faɗin jihar sun ci gaba da karɓar shirin hannu bibbiyu, inda iyaye da masu kula da yara suka bayyana cewa sun lura da ingantuwar lafiyar yaransu bayan karɓar maganin.

Haka kuma, Cibiyar Binciken Lafiya ta Najeriya (NIMR) na sa ido tare da tantance tasirin shirin wajen tabbatar da cewa duk wani mataki na gaba zai kasance bisa hujjojin kimiyya.

Masu ruwa da tsaki sun ce haɗin gwiwar gwamnati, ma’aikatan lafiya, abokan hulɗar ci gaba da al’ummomi na ƙara wa jama’a kwarin gwiwa kan shirin, tare da ƙarfafa ƙoƙarin rage mutuwar yara da za a iya kauce wa a jihar Yobe.

Afrika, Kimiya, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi
Next Post: ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.