Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau
Published: July 7, 2026 at 12:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Bauchi ta kama wasu matasa biyu da ake zargi da hannu a wani harin fashi da makami da fasa gida da ya faru a garin Gadau da ke ƙaramar hukumar Gamawa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na safiyar ranar 8 ga Yunin 2026, lokacin da wasu mutane biyar dauke da adda da sauran makamai masu haɗari suka kutsa cikin gidan wani matashi mai shekaru 28.

A cewar rundunar, maharan sun balle ƙofar ɗakin kwanan mamacin, tare da yi masa da matarsa barazana da makamai kafin su ɗaure su, sannan suka sace babur ƙirar Jincheng, wayoyin salula na Android guda biyar, atamfofi guda goma, agogon hannu guda uku, hula ɗaya da kuɗi Naira miliyan ɗaya. An kiyasta darajar kayan da aka sace ta kai kusan Naira miliyan huɗu.

Bayan samun rahoton lamarin a ranar 3 ga Yulin 2026, jami’an ‘yan sanda sun fara bincike na sirri wanda ya kai ga kama Salisu Umar da Sadiq Shehu, dukkansu masu shekaru 20.

Sanarwar ta ce yayin gudanar da tantance waɗanda ake zargi, matar wanda aka yi wa fashin ta gano tare da nuna Sadiq Shehu a matsayin ɗaya daga cikin maharan da suka shiga ɗakinta tare da tilasta mata buɗe ƙofar gida domin sauran abokan aikinsa su shiga.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yaba wa jami’an ofishin ‘yan sanda na Gadau bisa nasarar da suka samu, tare da bayar da umarnin miƙa binciken zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike.

Ya kuma tabbatar da cewa rundunar na ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.

Haka kuma ya buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaƙi da aikata laifuka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara
Next Post: Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Chadi Ta Sauyawa ‘Yan Gudun Hijira Matsuguni Afrika
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
  • Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
  • An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba Afrika
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
  • Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.