Rundunar ‘Yan Sandan jihar Bauchi ta kama wasu matasa biyu da ake zargi da hannu a wani harin fashi da makami da fasa gida da ya faru a garin Gadau da ke ƙaramar hukumar Gamawa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar.
Sanarwar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na safiyar ranar 8 ga Yunin 2026, lokacin da wasu mutane biyar dauke da adda da sauran makamai masu haɗari suka kutsa cikin gidan wani matashi mai shekaru 28.
A cewar rundunar, maharan sun balle ƙofar ɗakin kwanan mamacin, tare da yi masa da matarsa barazana da makamai kafin su ɗaure su, sannan suka sace babur ƙirar Jincheng, wayoyin salula na Android guda biyar, atamfofi guda goma, agogon hannu guda uku, hula ɗaya da kuɗi Naira miliyan ɗaya. An kiyasta darajar kayan da aka sace ta kai kusan Naira miliyan huɗu.
Bayan samun rahoton lamarin a ranar 3 ga Yulin 2026, jami’an ‘yan sanda sun fara bincike na sirri wanda ya kai ga kama Salisu Umar da Sadiq Shehu, dukkansu masu shekaru 20.
Sanarwar ta ce yayin gudanar da tantance waɗanda ake zargi, matar wanda aka yi wa fashin ta gano tare da nuna Sadiq Shehu a matsayin ɗaya daga cikin maharan da suka shiga ɗakinta tare da tilasta mata buɗe ƙofar gida domin sauran abokan aikinsa su shiga.
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yaba wa jami’an ofishin ‘yan sanda na Gadau bisa nasarar da suka samu, tare da bayar da umarnin miƙa binciken zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike.
Ya kuma tabbatar da cewa rundunar na ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.
Haka kuma ya buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaƙi da aikata laifuka.


