Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau
Published: July 7, 2026 at 12:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Bauchi ta kama wasu matasa biyu da ake zargi da hannu a wani harin fashi da makami da fasa gida da ya faru a garin Gadau da ke ƙaramar hukumar Gamawa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na safiyar ranar 8 ga Yunin 2026, lokacin da wasu mutane biyar dauke da adda da sauran makamai masu haɗari suka kutsa cikin gidan wani matashi mai shekaru 28.

A cewar rundunar, maharan sun balle ƙofar ɗakin kwanan mamacin, tare da yi masa da matarsa barazana da makamai kafin su ɗaure su, sannan suka sace babur ƙirar Jincheng, wayoyin salula na Android guda biyar, atamfofi guda goma, agogon hannu guda uku, hula ɗaya da kuɗi Naira miliyan ɗaya. An kiyasta darajar kayan da aka sace ta kai kusan Naira miliyan huɗu.

Bayan samun rahoton lamarin a ranar 3 ga Yulin 2026, jami’an ‘yan sanda sun fara bincike na sirri wanda ya kai ga kama Salisu Umar da Sadiq Shehu, dukkansu masu shekaru 20.

Sanarwar ta ce yayin gudanar da tantance waɗanda ake zargi, matar wanda aka yi wa fashin ta gano tare da nuna Sadiq Shehu a matsayin ɗaya daga cikin maharan da suka shiga ɗakinta tare da tilasta mata buɗe ƙofar gida domin sauran abokan aikinsa su shiga.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yaba wa jami’an ofishin ‘yan sanda na Gadau bisa nasarar da suka samu, tare da bayar da umarnin miƙa binciken zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike.

Ya kuma tabbatar da cewa rundunar na ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere, yana mai jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.

Haka kuma ya buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaƙi da aikata laifuka.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara
Next Post: Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84 Afrika
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
  • Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.