Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”
Published: December 1, 2025 at 5:47 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukaci cikakken hadin kai da jarumta domin shawo kan matsalolin tsaro da na tattalin arziki da ke kara ta’azzara a Arewacin Najeriya.

Da yake jawabi a taron hadin gwiwar Kungiyar Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa a Kaduna, Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada bukatar daukar matakan da suka dace domin kare makomar yankin.

Ya nuna damuwa kan karuwar sace-sacen jama’a a jihohin Kebbi, Kwara, Kogi, Kano, Niger da Sokoto, da kuma sake tashin rikicin Boko Haram a Borno da Yobe, yana mai cewa wadannan hare-hare sun zamo babbar barazana ga zaman lafiya da wanzuwar cigaba.

Gwamnan ya jajanta wa iyalai da abin ya rutsa da su da gwamnatocin jihohin da abin ya shafa, tare da yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan gaggawar kubutar da wasu daga cikin daliban da aka sace.

Ya kuma tabbatar da goyon bayan kungiyar ga ci gaba da kokarin ceto sauran wadanda ke hannun masu garkuwa da mutane.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi gargaɗi kan jefa siyasa ko addini da kabilanci a cikin matsalar tsaro, yana mai cewa wannan rikici ya shafi kowa ba tare da bambanci ba.

Kan an danganta tsanantar matsalolin tsaro da talauci, jahilci, sauyin yanayi da rashin ingantattun ababen more rayuwa, yana mai cewa zaman lafiya ba zai tabbata ba sai an zuba jari a bangaren ci gaban dan Adam da tattalin arziki.

Daya daga cikin mahimman batutuwan taron shi ne yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Arewacin kasar.

Ya bukaci shugabannin Arewa su dauki matakin gaggawa da na hadin kai don magance matsalar.

Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada matsayar Arewa na goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi domin magance ta’azzarar tsaro a yankin.

Ya yaba wa shugaban kasa kan umarnin da ya bai wa Majalisar Dattawa da ta Wakilai da su hanzarta gyaran kundin tsarin mulki domin aiwatar da wannan manufar.

Ya kara jaddada cewa samun dorewar zaman lafiya ya dogara ne kan hadin gwiwar kowane sashi na al’umma sarakunan gargajiya a matsayin masu sulhu, malaman addini a matsayin masu yada zaman lafiya, shugabannin siyasa a matsayin masu gina ci gaba ba rarrabuwa ba. Hukumomin tsaro masu aiki cikin hikima, alkalan kotuna masu hanzarta hukunci da kuma al’umma a matsayin abokan hadin gwiwa wajen tsaron yankuna.

Tun Farko, a jawabinsa na maraba, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya ce Arewa na fuskantar babban kalubale na tsaro, tattalin arziki da zamantakewa wanda ke bukatar hadin kai da sabbin dabaru.

Ya jinjinawa takwarorin sa kan ci gaba da karfafa tattaunawa da aiki tare, yana mai cewa hakan ne kadai hanyar samun dorewar zaman lafiya da ci gaba a yankin.

Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa kuma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya yaba wa kungiyar karkashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya kan himmar da ta ke nuna wa wajen shawo kan manyan matsalolin da ke addabar Arewa.

Ya ce sarakunan gargajiya da malaman addini na goyon bayan wannan kokari, musamman tattaunawa da aka dade ana yi domin magance matsalolin tsaro, karfafa hadin kai da inganta walwalar al’umma.

Ya bukaci gwamnonin Arewa da su ci gaba da zama tsintsiya madaurin ki daya wajen samar da ingantattun hanyoyin dawo da kwanciyar hankali da ci gaba a yankin.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa
Next Post: Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
Gombe Ta Yi Fice A Duniya: Maryam Dan’azumi Ta Lashe Gasar Alƙur’ani Na Ƙasa Da Ƙasa Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.