Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci
Published: December 1, 2025 at 8:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Gwamnonin Arewacin Najeriya, sun kaddamar da Asusun tsaro a yankin, Inda kowacce jiha za ta ba da Biliyan ɗaya duk wata.

Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya tare da sarakunan gargajiya sun sanar da kafa Asusun tsaro na yankin Arewa, wanda kowace jiha da kananan hukumomin ta za su riƙa ba da naira biliyan ɗaya a duk wata domin magance matsanancin tsaro a yankin.

Sanarwa mai dauke da sa hannun Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan jihar Gombe, kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa ta bayyana cewa, wannan na cikin muhimman matsaloli da aka cimma a ƙarshen taron haɗin gwiwar Kungiyar Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewacin Najeriya, da aka gudanar a ranar Litinin a gidan Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna.

Taron ya samu halartar dukkan gwamnonin jihohin Arewa guda goma sha tara (19) da shugabannin majalisun gargajiya na kowacce jiha.

A yayin taron an tattauna kan manyan batutuwa da suka shafi yankin da Najeriya baki ɗaya, inda aka yanke waɗannan muhimman shawarwari.

Gaisuwar ta’aziyya ga jihohin da hare hare suka shafa. Gwamnonin sun yi jaje ga gwamnatoci da al’ummomin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sakkwato, Jigawa da Kano bisa kashe-kashe da sace sacen ‘yan makaranta da al’umma da aka yi a kwanakin baya haka kuma an miƙa ta’aziyya ga waɗanda hare-haren Boko Haram suka rutsa da su a Borno da Yobe.

Dakatar da hakar ma’adanai na wucin gadi:

Gwamnonin sun nuna damuwa kan yadda hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke kara haifar da matsalolin tsaro a Arewacin kasar a saboda haka sun bukaci shugaban ƙasa ya umarci Ministan Ma’adanai ya dakatar da dukkan hakar ma’adanai na watanni shida, domin gudanar da cikakken bincike da tantance lasisin hako ma’adanai tare da hadin gwiwar gwamnonin jihohi.

Kafa Asusun Tsaro na Yanki:

A wani muhimmin mataki, kungiyar ta amince da kafa asusun tsaro na Yankin Arewa, wanda za a rika ba da naira biliyan ɗaya daga kowace jiha da kananan hukumomi duk wata, domin sauƙaƙa yaki da kalubalen tsaro.

Sannan tattaunawar ta amince a sake gudanar da wani taro a wani lokaci da za a sanar nan gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”
Next Post: Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota

Karin Labarai Masu Alaka

GOSEMA Ta Horar Da Mambobin LEMCs A Jihar Gombe Afrika
Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Bukaci Al’ummar Gombe Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Ta’addanci Afrika
Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
Gombe Ta Ƙarfafa Ilimin Almajirai Da Tsangaya Don Rage Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba Amurka
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • Lawanti Ya Ƙara Wa Gombe Daraja A Fannin Aikin Jarida – NUJ Afrika
  • Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
  • Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
  • Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.