Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci
Published: December 1, 2025 at 8:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Gwamnonin Arewacin Najeriya, sun kaddamar da Asusun tsaro a yankin, Inda kowacce jiha za ta ba da Biliyan ɗaya duk wata.

Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya tare da sarakunan gargajiya sun sanar da kafa Asusun tsaro na yankin Arewa, wanda kowace jiha da kananan hukumomin ta za su riƙa ba da naira biliyan ɗaya a duk wata domin magance matsanancin tsaro a yankin.

Sanarwa mai dauke da sa hannun Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan jihar Gombe, kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa ta bayyana cewa, wannan na cikin muhimman matsaloli da aka cimma a ƙarshen taron haɗin gwiwar Kungiyar Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewacin Najeriya, da aka gudanar a ranar Litinin a gidan Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna.

Taron ya samu halartar dukkan gwamnonin jihohin Arewa guda goma sha tara (19) da shugabannin majalisun gargajiya na kowacce jiha.

A yayin taron an tattauna kan manyan batutuwa da suka shafi yankin da Najeriya baki ɗaya, inda aka yanke waɗannan muhimman shawarwari.

Gaisuwar ta’aziyya ga jihohin da hare hare suka shafa. Gwamnonin sun yi jaje ga gwamnatoci da al’ummomin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sakkwato, Jigawa da Kano bisa kashe-kashe da sace sacen ‘yan makaranta da al’umma da aka yi a kwanakin baya haka kuma an miƙa ta’aziyya ga waɗanda hare-haren Boko Haram suka rutsa da su a Borno da Yobe.

Dakatar da hakar ma’adanai na wucin gadi:

Gwamnonin sun nuna damuwa kan yadda hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke kara haifar da matsalolin tsaro a Arewacin kasar a saboda haka sun bukaci shugaban ƙasa ya umarci Ministan Ma’adanai ya dakatar da dukkan hakar ma’adanai na watanni shida, domin gudanar da cikakken bincike da tantance lasisin hako ma’adanai tare da hadin gwiwar gwamnonin jihohi.

Kafa Asusun Tsaro na Yanki:

A wani muhimmin mataki, kungiyar ta amince da kafa asusun tsaro na Yankin Arewa, wanda za a rika ba da naira biliyan ɗaya daga kowace jiha da kananan hukumomi duk wata, domin sauƙaƙa yaki da kalubalen tsaro.

Sannan tattaunawar ta amince a sake gudanar da wani taro a wani lokaci da za a sanar nan gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”
Next Post: Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe Afrika
Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Ga Watan Ramadan A Najeriya Da Nijar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
  • Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi Afrika
  • Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.