Gwamnatin jihar Gombe ta sake jaddada ƙudirin ta na rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, ta hanyar bullo da dabarun da za su inganta yawan ɗaliban da ke shiga makarantun gwamnati a dukkan matakan karatu.
Kwamishiniyar Ilimi ta jihar, Mataimakiyar Farfesa Aishatu Umar Maigari, ta bayyana hakan ne a wani taron tuntubar masu ruwa da tsaki kan ilimin Almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta, wanda aka gudanar a Gombe.
Kwamishiniyar, wadda Sakataren Dindindin na ma’aikatar, Alhaji Abubakar Hassan, ya wakilta, ta ce ma’aikatar, tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyi da hukumomin da abin ya shafa, na yin ƙoƙari daga matakin ƙananan hukumomi da al’umma wajen magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta.
Ta ce kafa shirin Gombe State Basic Education and Skills Transformation, GO-BEST, na daga cikin matakan da gwamnatin jihar ta ɗauka domin inganta ingancin ilimi da kuma ƙara yawan ɗaliban da ke shiga makarantu.
Mataimakiyar Farfesa Aishatu Maigari ta ƙara da cewa, Hukumar Almajirai da Tsangaya ta jihar Gombe ma na taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ilimin Almajirai, musamman ta hanyar horaswa, sake horaswa da kuma ba malamai takardun shaidar da aka amince da su.
Ta yaba wa waɗanda suka shirya taron, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da bayar da goyon baya wajen magance matsalolin da ke kawo cikas ga harkar ilimi.
Tun da farko, Mai Bai wa Ministan Ilimi Shawara na Musamman kan Ilimin Almajirai da Yaran da Ba sa Zuwa Makaranta, Dakta Balarabe Shehu Kakale, ya ce gudanar da shirin a jihar Gombe ya samo asali ne sakamakon matakan da gwamnatin Gombe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta ɗauka wajen bunƙasa ilimin Almajirai da Tsangaya.
Dakta Kakale ya bayyana cewa, gina makarantun Tsangaya da Almajirai, da kuma kafa hukumar da ke kula da harkar, na daga cikin matakan da za su taimaka wajen hanzarta samun ci gaba a fannin.
Ya kuma gabatar da wasu takardu da aka amince da su, da kuma dokoki da sanarwar gwamnati da ke goyon bayan ilimin Almajirai, Tsangaya da Nomadic a Najeriya.
A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Ilimi ta Bai Ɗaya ta Jihar Gombe, SUBEB, Farfesa Hassan Bello, ya bayyana taron a matsayin wanda ya zo a kan lokaci.
Ya ce hukumar na aiki kafada da kafada da Ma’aikatar Ilimi ta jihar da Hukumar Almajirai da Tsangaya wajen tsara shirye-shiryen da za su inganta ilimin Almajirai da kuma rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.
Farfesa Hassan Bello ya buƙaci mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tallafa wa shirin, domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Sauran waɗanda suka gabatar da jawabai sun haɗa da Mai Bai wa Gwamnan Jihar Gombe Shawara kan Ilimin Almajirai da Tsangaya, Sayyada Aminatu Dahiru Usman Bauchi; Sakataren Janar na Jama’atu Nasril Islam, Alhaji Sale Danburam; Shugaban Kwalejin A.D. Rufai College of Education, Legal and General Studies, Misau, Dakta Muhammad Mujtapha Abdulkadir; da Kodinetan Hukumar Ilimin Manyan Mutane ta Ƙasa a Jihar Gombe, Mista Thauya Elkesa.
Sun bayyana cewa shirin zai taimaka matuƙa wajen magance matsalolin da ke hana yara samun ilimi, tare da tabbatar da goyon bayansu ga shirin.
Taron ya samu halartar malamai da masana, ciki har da Goni Alaramma Mai Babban Allo, Goni Musa Checheniya, wakilan FOMWAN reshen Gombe, Sakatariya Rabia da Sheikh Yahaya Bello, da sauran masu ruwa da tsaki.
Mahalarta taron sun jaddada muhimmancin haɗin gwiwar gwamnati, malamai, iyaye, kungiyoyin addini da sauran masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da cewa yara sun samu damar zuwa makaranta da kuma samun ingantaccen ilimi.


