Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
Published: April 14, 2026 at 8:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta yi karin haske kan harin nan da jiragen yakin Rundunar Sojin Sama ta Kasa (NAF) suka kai a yankin Jilli na Karamar Hukumar Gubio, Jihar Borno, ranar 11 ga Afrilu, 2026.

Gwamnati ta bayyana cewa harin ba na kan-mai-uwa da wabi ba ne; an kai shi ne kai-tsaye kan maboyar ’yan ta’adda.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a a Najeriya Mohammed Idris ya jaddada cewa harin na karkashin Operation HADIN KAI ne, kuma an gudanar da shi ne bayan samun kwararan hujjoji na sirri.

Wannan yanki na Jilli, wanda aka fi sani da Kasu Daulaye (Kasuwar ’yan ta’adda), ya dade yana karkashin ikon mayakan Boko Haram da ISWAP. A nan ne suke Karbar haraji a hannun jama’a, Siyan kayayyakin bukata, da Shirya yadda za su kaddamar da hare-hare.

Sanarwar ta kara da cewa, a ranar 12 ga Afrilu, sojoji sun kama wani matashi mai shekara 15 mai suna Tijjani a yankin Ngamdu. Tijjani ya amsa cewa shi ne yake kai wa ’yan ta’addan ISWAP kudi da sauran kayayyaki a tsakanin Jilli da wasu wurare, lamarin da ya nuna yadda mahukuntan ke amfani da kananan yara wajen aikata barna.

Haka zalika, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya tabbatar da cewa tun shekaru biyar da suka gabata aka rufe kasuwannin Jilli da Gazabure saboda yadda ’yan ta’adda suka mamaye su.

Duk da cewa gwamnati ta kare matakin sojoji, ta mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda abin ya shafa. Ministan ya bayyana cewa:

“Rayuwar kowane dan Najeriya tana da muhimmanci, kuma muna matukar da na sani kan asarar rayukan farar hula da aka samu.”

Domin tabbatar da gaskiya da adalci, Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin gudanar da bincike mai zaman kansa kan yadda aka tsara harin da kuma inda aka samu kuskure.

A yanzu haka, gwamnati tana hada gwiwa da hukumomin agaji na NEMA da SEMA domin kai dauki ga iyalai da wadanda suka jikkata a jihohin Borno da Yobe.

Gwamnati ta bukaci fararen hula da su kiyaye shiga yankunan da aka sanya wa takunkumi, su kuma ci gaba da ba jami’an tsaro hadin kai domin kawo karshen wannan fitina.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya
Next Post: Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Karin Labarai Masu Alaka

Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC Afrika
Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.