Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua
Published: December 29, 2025 at 11:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dan wasan dambe na kasar Birtaniya, Anthony Joshua ya yi hatsarin mota a jihar Ogun da ke Nigeria, hatsarin ya yi sanadiyar rayukan mutane biyu, a cewar ‘yan sanda ranar Litinin.

‘Yan sandan na jihar Ogun sun ce motar su Anthony Joshua ta yi karo ne da wata motar, kuma An kai shi asibiti, inda suka kara da cewa suna gudanar da bincike kan dalilin faruwar hatsarin.

Hukumar kiyaye hadura ta kasa ta ce mutane biyar ne hatsarin ya rutsa da su a hanyar Lagos-zuwa Ibadan, inda Joshua ya samu raunuka kadan, mutum biyu suka mutu, wasu biyu kuma ba su samu rauni ko kadan ba.

Hukumar ta ce, farkon bincike ya nuna motar da take dauke da Mr. Joshua tana zura gudu ne sai kan motar ya kwace, yayin da take kokarin wuce wata mota, da tayi karo da wata gingimari da ke ajiye a gefen titi.

Anthony Joshua, wanda ya kasance iyayen sa ‘yan Nigeria ne da Birtaniya, ya yi makarantar kwana ne a garin Ikenne, wanda ya ke mil 53 daga inda hatsarin ya faru, kafin daga bisani ya koma Birtaniya yana da shekara 12.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan
Next Post: Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika
Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
  • Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.