Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi
Published: February 2, 2026 at 5:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kakakin majalisar wakilai na kasar Amurka Mike Johnson ya shiga tsaka mai wuya, wajen kokarin ganin kasafin kudin da aka tsara ya samu wucewa, saboda kaucewa durkusar da ayyukan gwamnati na wani bangare zuwa lokaci me tsawo, bayan da takkadama ta yi tsanani tsauraran dokokin da shugaba Donald Trump ya sa kan shige da fice.

Johnson ya ce ya dogara ga taimako daga Trump don ganin an zartar da kasafin. Trump a nasa bangaren ya cimma yarjejeniya da ‘yan majalisar dattawa don cire kasafin kudin da za’a yi amfani da shi a ma’aikatar tsaron cikin gida daga sauran gundarin kasafin, bayan da jama’a suka nuna fushin su kan kisan mutane biyu yayin gudanar da zanga-zangar adawa ga Jami’an shige da fice a jihar Minnesota.

A yarjejeniyar, za’a bawa ma’aikatar tsaron cikin gida kudi na kankanin lokaci zuwa 13 ga wannan watan, wannan ya bawa majalisar kasa wa’adi ta yi kokari ta samo matsaya daya kan sababbin iyakokin da za’a gindaya kan aikin jami’an shige da fice da aka fi sani da ICE.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda
Next Post: Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.